Connect with us

Labarai

Jami’an Hukumar Hana Shige Da Fice Na Iya Nasu Kokari a Kabi

Published

on

An Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Kula Da Jin Dadin Jami’an Da Ke Aiki Akan Iyakokin Kasan nan

 

Shugaban Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa, Kemi Nandap, ta yi kira ga shugaban kasa Bola Tinubu da ya kawo wa hukumar agajin jin dadin jami’an da ke kan iyaka saboda rashin matsuguni na kawo tsaiko wajen gudanar da aikinsu yadda ya kamata.

 

Kwanturola Janar din ta bayyana hakan ne a Kebbi a lokacin da take tantance kan iyakokin jihar domin duba halin da ma’aikatanta ke ciki da kuma kalubalen da ma’aikatanta ke fuskanta a kan iyakokin jihar.

 

Ta kuma jaddada bukatar tabbatar da tsaro a kan iyakokin kasar, domin a sa ido kan abubuwan da ke shigowa daga wajen kasar.

 

“Mun ziyarci kan iyakokin kasa da na ruwa a Kamba, Lolo da Dolekaina, abin da muka gani yana da kyau amma akwai bukatar a yi aiki sosai don tabbatar da tsauraran kan iyakokin, Kebbi wuri ce da ta yi iyaka da kasashe biyu shi ya sa ya zama dole mu yi aiki tukuru.

 

Nandap ta bayyana cewa, suna aiki ba dare ba rana don ƙaddamar da aikin amfani da na’urar zamani e-border wanda zai taimaka wajen bada takardun shige da fice cikin sauki.

 

Ta yabawa kwamandan rundunar dake jihar Kebbi a karkashin kulawar Kwanturola Saidu Muhammed Sabo, bisa yadda hukumar take gudanar da aikinta.

COV/Abdullahi Tukur/Wababe

Labarai

Labarai19 hours ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi20 hours ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai20 hours ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai22 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai2 days ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai3 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai3 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai3 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Mafi Shahara