Labarai
Jami’an Hukumar Hana Shige Da Fice Na Iya Nasu Kokari a Kabi
An Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Kula Da Jin Dadin Jami’an Da Ke Aiki Akan Iyakokin Kasan nan
Shugaban Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa, Kemi Nandap, ta yi kira ga shugaban kasa Bola Tinubu da ya kawo wa hukumar agajin jin dadin jami’an da ke kan iyaka saboda rashin matsuguni na kawo tsaiko wajen gudanar da aikinsu yadda ya kamata.
Kwanturola Janar din ta bayyana hakan ne a Kebbi a lokacin da take tantance kan iyakokin jihar domin duba halin da ma’aikatanta ke ciki da kuma kalubalen da ma’aikatanta ke fuskanta a kan iyakokin jihar.
Ta kuma jaddada bukatar tabbatar da tsaro a kan iyakokin kasar, domin a sa ido kan abubuwan da ke shigowa daga wajen kasar.
“Mun ziyarci kan iyakokin kasa da na ruwa a Kamba, Lolo da Dolekaina, abin da muka gani yana da kyau amma akwai bukatar a yi aiki sosai don tabbatar da tsauraran kan iyakokin, Kebbi wuri ce da ta yi iyaka da kasashe biyu shi ya sa ya zama dole mu yi aiki tukuru.
Nandap ta bayyana cewa, suna aiki ba dare ba rana don ƙaddamar da aikin amfani da na’urar zamani e-border wanda zai taimaka wajen bada takardun shige da fice cikin sauki.
Ta yabawa kwamandan rundunar dake jihar Kebbi a karkashin kulawar Kwanturola Saidu Muhammed Sabo, bisa yadda hukumar take gudanar da aikinta.
COV/Abdullahi Tukur/Wababe
-
Labarai4 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai2 days agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai6 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai5 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
