Ilimi
An Ceto Daliban Jami’ar Jihar Kogi Da Aka Sace
Jami’an tsaro sun ceto daliban da ’yan bindiga suka yi garkuwa da su a Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kogi.
Rundunar hadin gwiwar sojoji da sauran hukumomin tsaro ta ceto daliban su tara ne bayan musayar wuta da ’yan bindigar.
Rundunar Sojin Kasa ta Najeriya ta ce a samamen da suka kaddamar a Dajin Osara, yankin da jami’ar take, suka murkushe ’yan bindigar da suka sace daliban.
Sanarwar rundunar ta ranar Lahadi ta ce tserewa ’yan bindigar suka yi suka bar daliban, ganin cewa jami’an tsaron sun fi karkfinsu.
Rundunar ta ce sojoji sun kuma ceto wasu mutane 17 da aka sace a Karamar Hukumar Batsari ta Jihar Katsina.
An ceto mutanen ne bayan daukin da sojoji suka kai inda suka bi sawun ’yan bindigar da suka sace mutanen, suka yi musayar wuta tare da ceto mutanen bayan ’yan bindigar sun tsere.
A Jihar Zamfara ma sojoji sun ceto wasu mutane biyu da aka yi sace a kauyen Danzara da ke yankin karamar hukumar Maru.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
