Kasuwanci
Kasashen Afirka Na Taro Kan Ta’addanci A Abuja

An buɗe taron yini biyu kan yaƙi da ta’addanci a ƙasashen Afirka da ke gudana a Abuja, babban birnin Najeriya.
Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ne ya ƙaddamar da taron mai taken ‘ƙarfafa ayyukan haɗin kai tsakanin ƙasashe da bunƙasa hukumomi don murƙushe ta’addanci’.
An shirya taron domin ƙarfafa yaƙi da ta’addanci a tsakanin ƙasashen nahiyar Afirka ta hanyar haɗin kai na sojoji da daƙile kwararar makamai da kuɗade tsakanin ƙasashen da zummar tallafa wa masu aikata manyan laifuka.
Taron na zuwa ne yayin da ƙasashen Afirka da dama ke fuskantar barazanar tsaro daga ƙungiyoyin masu iƙirarhin jihadi da ƴan bindiga musamman a sassan yankin Sahel.
Shugabanin ƙasashe daga yankin da masana kan harkoki tsaro daga nahiyar da ɓangaren majalisar ɗinkin duniya ne za su halarci taron.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai19 hours agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai7 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai2 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
