Kasuwanci
Tinubu Yayi Sabbin Nade-Nade A Kasuwar Shinko Ta Kasa
Shugaba Bola Tinubu ya amince da nadin Mista Mairiga Aliyu Katuka a matsayin shugaban Hukumar kula da kasuwannin shinko na kasa.
Wata sanarwa da mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya fitar ta ce shugaban ya kuma nada Mista Emomotimi Agama a matsayin babban Darakta hukumar.
Frana Chukwuogor kuma an nada shi a matsayin Babban Kwamishinan kula da harkokin Shari’a.
Sai kuma Mista Bola Ajomale a matsayin Babban Kwamishinan kula da Ayyuka. Ita kuma Mrs. Samiya Hassan Usman a matsayin kwamishinar kula da harkokin hukumar.
Mista Lekan Belo kuwa a matsayin kwamishinan zartarwa. Da kuma Kasimu Garba Kurfi a matsayin Kwamishina.
Sanarwar ta kara da cewa, shugaba Tinibu ya bayyana kwarin gwiwar cewa dukkan mambobin hukumar za su yi amfani da kwarewarsu wajen ci gaba da aikin hukumar na samar da ingantacciyar kasuwa mai inganci, da gaskiya, ta yadda masu zuba jari za su samu kwarin gwiwa tare da bayar da gudummawa sosai ga harkokin kasuwanci. ci gaban tattalin arzikin kasa.
Bello Wakili/Wababe
-
Labarai4 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi5 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha5 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai5 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai5 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai3 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai5 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai5 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar