Labarai
Kotu ta Tsare Mutum 29 da Ake Zargi da Fafutukar Kafa Kasar Yarabawa
Kotun majistre ta Iyaganku da ke Ibadan ta bayar da umarnin a tsare mutum 29 da ake zargin masu fafutukar kafa ƙasar Yarabawa ne saboda yadda suka yi wa harabar sakatariyar jihar Oyo ƙawanya.
A ranar Laraba ne aka gurfanar da mutanen saboda zargin su da hannu a harim da suka kai kan sakatariyar da kuma ofishin gwamna da bai yi nasara ba.
A baya-bayan nan ne wasu mutane da suka rufe fuskarsu suka yi dirar mikiya a sakatariyar jihar inda suka kafa tutarsu kafin jami’an tsaro su tarwatsa su.
A cewar jaridar Vanguard, mutanen waɗanda ke fuskantar tuhume-tuhume bakwai kan haɗa baki da cin amanar ƙasa da kuma shiga haramtacciyar ƙungiya da riƙe makami cikin jama’a da kuma aikata abin da ka iya kawo barazana ga zaman lafiya da mallakar makami ba bisa ƙa’ida ba.
Mutanen da ake zargi, har da wata matashiya da manyan mata biyar, an tsare su a gidan gyaran hali da ke Ibadan bisa umarnin babban majistare, Olabisi Ogunkanmi.
Daga bisani kuma mai shari’ar ya ɗage sauraron ƙarar zuwa 1 ga watan Agusta.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
