Connect with us

Labarai

Gwamna Namadi Ya Kai Ziyarar Bazata Cibiyoyin Ciyar Da Abincin Azumi

Published

on

Gwamna Umar Namadi na Jihar Jigawa ya kai ziyarar bazata ga wuraren bayar da abinci na Ramadan a babban birnin jihar domin duba yadda ake aiwatar da shirin ciyarwar.

Wakilinmu ya ruwaito cewa Gwamnan ya ziyarci cibiyoyi a Dundubus, da Karnaya, da Kaci da Limawa, dukkaninsu a kewayen birnin Dutse.

Yayin bincikensa, Malam Umar Namadi ya yaba wa wasu cibiyoyi bisa jajircewarsu da kishin tabbatar da cewa shirin ciyarwar Ramadan yana tafiya yadda ya kamata.

Sai dai kuma, ya nuna matukar rashin jin dadinsa bayan gano wasu matsaloli na rashin iya tafiyar da shirin a wasu wuraren bayar da abincin.

Gwamnan ya jaddada bukatar kiyaye gaskiya, da adalci da tsafta a yayin rarraba abincin, yana mai kira ga masu ruwa da tsaki da su gyara duk wasu kura-kurai nan take.

Namadi ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da kokarin tabbatar da cewa dukkan cibiyoyin ciyarwa na Ramadan suna aiki yadda ya dace, tare da girmama mutuncin al’umma.

Ya kuma tabbatar da cewa za a dauki matakan da suka dace domin inganta yadda ake gudanar da shirin da kuma magance duk wasu matsaloli da aka gano.

Gwamnan ya kuma bukaci hukumomin yankuna da shugabannin al’umma da su kara kaimi wajen sa ido domin tabbatar da aiwatar da shirin cikin tsari.

Ya jaddada cewa jin dadin al’umma na daga cikin manyan abubuwan da gwamnatinsa ke ba muhimmanci.

Usman Muhammad Zaria 

Labarai

Labarai4 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai24 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara