Labarai
Gwamna Umar Namadi Ya Kara Karfafa Gwiwar Matasa Domin Ci Gaban Jihar Jigawa
Gwamna Umar Namadi ya jaddada kudirin gwamnatin jihar na ci gaba da kaddamar da ayyuka masu ma’ana don ci gaban jihar Jigawa.

Ya bada wannan tabbacin ne a wani taron jin ra’ayoyin jama’a a karamar hukumar Babura.

Malam Umar Namadi ya tunatar da matasa bukatar ganin sun kasance masu tarbiya da girmama na gaba da su, domin samun kyakkyawar rayuwa a gaba.

Shi ma da yake nasa jawabin, sakataren gwamnatin jihar, Malam Bala Ibrahim ya ce gwamnati mai ci a jihar ta bullo da shirin wayar da kan jama’a domin biyan bukatun jama’a da kuma sanya su cikin harkokin mulki.

Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, a yayin taron, sama da magoya bayan jam’iyyun PDP, da NNPP da SDP dubu daya da dari biyu ne suka sauya sheka zuwa jam’iyyar APC, bisa la’akari da nasarorin da gwamnatin mai ci ta yi a jihar.
Usman Muhammad Zaria
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
