Connect with us

Kasuwanci

Za Mu Taimaka Wajen Bunkasa Noma- Hon. Mustapha

Published

on

← Back

Thank you for your response. ✨

Shugaban kwamitin majalisar dattijai mai kula da ayyukan noma da raya karkara, Sanata Saliu Mustapha, ya Jaddada kudirinsa na tallafama yunkurin gwamnatin tarayya wajen bunkasa sashen noma don Samar da sana’o’i da wadata kasa da abinci.

Sanatan ay bayyana hakan ne yayi da yake kaddamar da rabon taki buhu 3,500 ga kananan manoma a da suka fito daga kananan hukumomi hudu dake mazabarsa ta Kwara ta tsakiya a Jihar Kwara.

Sanatan Salihu Mustapha, ya ce rabon kayan noman da suka hada da injection nan ban ruwa wani yunkuri ne a matakin farko na tabbatar da dorewar ayyukan noma a fadin gundumar dama Jihar baki daya.

Sanatan ya kara da cewa wadanda aka tsara suci gajiyar rabon kayan sun hada da mambobin kungiyar manoma ta Najeriya wato AFAN, mambobin kungiyoyin manoma na jam’iyyar APC da daidaikun jama’a dake sana’ar noma a mazabar tasa.

Da yake kaddamar da rabon kayayyakin noman a filin wasa na hukumar raya kogin Neja ta karamar hukumar Ilorin, Sanata Mustapha, ya ce akwai tunanin fadada shirin don ganin wasu karin manoma sunci gajiyar shirin a nan gaba kadan.

Yace shirin bada tallafin kayan noman mai taken “Tallafawa Manoman Kwara ta Tsakiya: Bude hanyoyin dogaro da kai wajen samar da abinci,” na da nufin tallafa ayyukan noma da habbaka samun yabanya ga manoman mazabar.

“Tasirin sauyin yanayi da kuma yawaitar noman gonaki yana da illa ga ingancin kasar noma. Wannan ya haifar da raguwar amfanin amfanin gonar da ake samu.

“Yana da mahimmanci in jaddada cewa ni da kaina na sayi buhunan taki guda 3,500 da aka raba a yau domin karfafa wa manomanmu gwiwa da inganta amfanin gonakinsu,” in ji Sanata Mustafa.

Mustapha ya bayyana cewa rabon taki mai yawa irin wannan na nuni da yadda ake zuba jari mai yawa a fannin noma, wanda hakan ke nuna aniyar inganta samar da abinci da tallafawa rayuwar manoma domin bunkasa noman abinci a jihar.

Sanatan na Kwara ya yi amfani da wannan dama wajen nuna wasu daga cikin nasarorin da ya samu cikin shekara daya da shafe a matsayinsa na dan majalisa da ya hada da gudanar da aikin sake gina titi Mai tsawon kilomita daya a daura da Jami’ar Al-Hikmah wanda ya dangana da titin Oke zuwa Foma a karamar hukumar Ilorin ta yamma.

Ya kara da cewa, an kuma gina rijiyoyin burtsatse masu amfani da hasken rana da sanya fitulun titi a fadin kananan hukumomin hudu na mazabar domin taimakawa kokarin gwamnatin jihar na ganin jama’a sun samu tsaftataccen ruwan sha.

REL : TSIBIRI

Labarai

Labarai11 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara