Kasuwanci
Za Mu Taimaka Wajen Bunkasa Noma- Hon. Mustapha
Shugaban kwamitin majalisar dattijai mai kula da ayyukan noma da raya karkara, Sanata Saliu Mustapha, ya Jaddada kudirinsa na tallafama yunkurin gwamnatin tarayya wajen bunkasa sashen noma don Samar da sana’o’i da wadata kasa da abinci.
Sanatan ay bayyana hakan ne yayi da yake kaddamar da rabon taki buhu 3,500 ga kananan manoma a da suka fito daga kananan hukumomi hudu dake mazabarsa ta Kwara ta tsakiya a Jihar Kwara.
Sanatan Salihu Mustapha, ya ce rabon kayan noman da suka hada da injection nan ban ruwa wani yunkuri ne a matakin farko na tabbatar da dorewar ayyukan noma a fadin gundumar dama Jihar baki daya.
Sanatan ya kara da cewa wadanda aka tsara suci gajiyar rabon kayan sun hada da mambobin kungiyar manoma ta Najeriya wato AFAN, mambobin kungiyoyin manoma na jam’iyyar APC da daidaikun jama’a dake sana’ar noma a mazabar tasa.
Da yake kaddamar da rabon kayayyakin noman a filin wasa na hukumar raya kogin Neja ta karamar hukumar Ilorin, Sanata Mustapha, ya ce akwai tunanin fadada shirin don ganin wasu karin manoma sunci gajiyar shirin a nan gaba kadan.
Yace shirin bada tallafin kayan noman mai taken “Tallafawa Manoman Kwara ta Tsakiya: Bude hanyoyin dogaro da kai wajen samar da abinci,” na da nufin tallafa ayyukan noma da habbaka samun yabanya ga manoman mazabar.
“Tasirin sauyin yanayi da kuma yawaitar noman gonaki yana da illa ga ingancin kasar noma. Wannan ya haifar da raguwar amfanin amfanin gonar da ake samu.
“Yana da mahimmanci in jaddada cewa ni da kaina na sayi buhunan taki guda 3,500 da aka raba a yau domin karfafa wa manomanmu gwiwa da inganta amfanin gonakinsu,” in ji Sanata Mustafa.
Mustapha ya bayyana cewa rabon taki mai yawa irin wannan na nuni da yadda ake zuba jari mai yawa a fannin noma, wanda hakan ke nuna aniyar inganta samar da abinci da tallafawa rayuwar manoma domin bunkasa noman abinci a jihar.
Sanatan na Kwara ya yi amfani da wannan dama wajen nuna wasu daga cikin nasarorin da ya samu cikin shekara daya da shafe a matsayinsa na dan majalisa da ya hada da gudanar da aikin sake gina titi Mai tsawon kilomita daya a daura da Jami’ar Al-Hikmah wanda ya dangana da titin Oke zuwa Foma a karamar hukumar Ilorin ta yamma.
Ya kara da cewa, an kuma gina rijiyoyin burtsatse masu amfani da hasken rana da sanya fitulun titi a fadin kananan hukumomin hudu na mazabar domin taimakawa kokarin gwamnatin jihar na ganin jama’a sun samu tsaftataccen ruwan sha.
REL : TSIBIRI
-
Kasuwanci7 days ago
PDP Katsina Ta Zabi Sabbin Shugabanni
-
Labarai6 days ago
Kamfanin Mai Na Kasa Na Fuskantar Matsalolin Kudaden Samar Da Man Fetur
-
Labarai6 days ago
Gwamna Lawal Ya Yi Sabon Nadi Ga Hukumar Asusun Kula Da Harkokin Tsaro
-
Kasuwanci6 days ago
Gwamnatin Tarayya Ta Fara Gina Rukunan Gidaje 500 A Kano
-
Labarai5 days ago
Shugaba Bola Tinubu Ya Jajantawa Iyalan Yar’Adua Bisa Rasuwar Hajiya Dada
-
Labarai7 days ago
Ku Gaggauta Kammala Ayukkan Da Ke Hannun Ku A Arewa Maso Gabas
-
Labarai3 days ago
ACF Ta Ce Babban Kalubalen Arewa Yanzu Shi Ne Rashin Tsaro
-
Labarai6 days ago
APC Ta Lashe Dukkan Kujerun Kansiloli Da Kansiloli A Kebbi