Connect with us

Labarai

Za a samu jinkirin saukar damina a wasu jihohin Najeriya- Nimet

Published

on

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi hasashen cewa za a samu jinkirin saukar damina a wasu sassan ƙasar musamman jihohin yankin arewa ta tsakiya.

Ministan kula da harkokin sufurin jiragen sama da sararin samaniyar ƙasar, Festus Keyamo ne ya bayyana haka a lokacin fitar da rahoton hasashen da hukumar Nimet ta saba fitarwa na duk shekara.

Rahoton ya ce jihohin yankunan ƙasar da dama za su gamu da matsalar ɗaukewar damunar da wuri a bana.

Sai dai kuma hukumar ta NIMET ta ce, za kuma a samu saukar ruwan saman da wuri a jihohin Borno da Abiya da kuma Akwa Ibom saɓanin yadda aka saba gani.

Hasashen ya nuna cewa, za a samu ɗaukewar ruwan sama da wuri a jihohin Kano da Jigawa da Sokoto da Kebbi da kuma Kaduna a yankin arewa maso yamma.

Sai kuma Bauchi da Gombe da Yobe da Taraba a yankin Arewa maso gabas. Akwai kuma Filato da Nasarawa a yankin arewa maso tsakiya.

Sannan jihohin Legas da Ogun a kudu maso yamma da kuma Cross River a kudu maso kudu, da Ebonyi a kudu masu gabashin Najeriyar.

Sai dai kuma hasashen hukumar kula da yanayin ta Najeriya , NIMET ya nuna cewa wasu jihohin kasar za su iya samun saukar damina kamar yadda suka saba gani inda kuma za su samu ruwan sama kaman yadda suka saba samu a shekara.

Labarai

Labarai10 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara