Connect with us

Labaran Ketare

‘Yan Ta’adda Sun Sace Kananan Yara Sama Da 70 A Mozambique

Published

on

Kananan yara fiye da 70 ne ake fargabar bacewarsu a yankin Cabo Delgado na Mozambique bayan wasu sabbin hare-haren mayakan jihadi masu biyayya ga kungiyar IS, wanda zuwa yanzu ya tilastawa mutane fiye da dubu 100 barin muhallansu.

Kungiyoyin agaji da suka kunshi Save the children da kuma MSF na ci gaba da kokawa game da yadda hare-haren ‘yan ta’addan na Mozambique ke ci gaba da lakume rayukan kananan yara inda zuwa yanzu suka tilasta kulle makarantu 129 kamar yadda wani rahoton Majalisar Dinkin Duniya ke bayyanawa.

 

Mahukuntan Mozambique sun tabbatar da hare-haren a arewacin Cabo Delgado duk da cewa basu fitar da cikakkun alkaluman kananan yaran ba, amma sun ce adadin wadanda aka raba su da iyayensu tare da tasa keyarsu cikin dazuka ya haura 70.

A cewar mahukuntan a makwannin baya-bayan nan ne hare-haren ‘yan ta’addan ya sake tsananta inda daga karshen watan Janairu zuwa yanzu, suka raba iyalai fiye da dubu 100 da muhallansu, hare-haren da suka faro tun a shekarar 2017.

 

Majalisar Dinkin Duniya ta ce fiye da kashi 60 na wadanda hare-haren ya fi yiwa illa kananan yara ne kuma adadin na harin baya-bayan nan shi ne mafi yawa da ‘yan ta’addan na Mozambique suka taba kwashewa ta fuskar kananan yara.

 

Akwai dai rahotanni masu alaka da cin zarafi baya ga zartas da hukuncin kisa bisa zalinci da ‘yan ta’addan na Mozambique ke yi kan kananan yara ciki har da wadanda suka sata.

 

 

 

 

Labarai

Labarai7 minutes ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai2 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai23 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai2 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Mafi Shahara