Labaran Ketare
‘Yan Ta’adda Sun Sace Kananan Yara Sama Da 70 A Mozambique

Kananan yara fiye da 70 ne ake fargabar bacewarsu a yankin Cabo Delgado na Mozambique bayan wasu sabbin hare-haren mayakan jihadi masu biyayya ga kungiyar IS, wanda zuwa yanzu ya tilastawa mutane fiye da dubu 100 barin muhallansu.
Kungiyoyin agaji da suka kunshi Save the children da kuma MSF na ci gaba da kokawa game da yadda hare-haren ‘yan ta’addan na Mozambique ke ci gaba da lakume rayukan kananan yara inda zuwa yanzu suka tilasta kulle makarantu 129 kamar yadda wani rahoton Majalisar Dinkin Duniya ke bayyanawa.
Mahukuntan Mozambique sun tabbatar da hare-haren a arewacin Cabo Delgado duk da cewa basu fitar da cikakkun alkaluman kananan yaran ba, amma sun ce adadin wadanda aka raba su da iyayensu tare da tasa keyarsu cikin dazuka ya haura 70.
A cewar mahukuntan a makwannin baya-bayan nan ne hare-haren ‘yan ta’addan ya sake tsananta inda daga karshen watan Janairu zuwa yanzu, suka raba iyalai fiye da dubu 100 da muhallansu, hare-haren da suka faro tun a shekarar 2017.
Majalisar Dinkin Duniya ta ce fiye da kashi 60 na wadanda hare-haren ya fi yiwa illa kananan yara ne kuma adadin na harin baya-bayan nan shi ne mafi yawa da ‘yan ta’addan na Mozambique suka taba kwashewa ta fuskar kananan yara.
Akwai dai rahotanni masu alaka da cin zarafi baya ga zartas da hukuncin kisa bisa zalinci da ‘yan ta’addan na Mozambique ke yi kan kananan yara ciki har da wadanda suka sata.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai23 hours agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai7 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai2 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
