Labarai
‘Yan Bindiga Sun Shiga Hannu Yayin Bai Wa Sojoji Cin Hanci A Taraba
Rundunar Sojin Najeriya a jihar Taraba ta ce dakarunta sun kame wasu ’yan bindiga da suka yi musu tayin cin hancin Naira miliyan biyu.
Mataimakin daraktan hulda da jama’a na Runduna ta Shida da ke Jalingo, Laftanar Oni Olubodunde ne ya sanar da kama wadanda ake zargin a kauyukan Chinkai da kuma Sarkin Kudu da ke kananan hukumomin Wukari da Ibbi a jihar.
Ya ce, sojojin sun yi nasarar cafke wasu ’yan ta’adda da suka nemi bayar da cin hancin Naira miliyan biyu domin a sake su.
Ya ce, sojojin sun ki amincewa su karbi cin hancin daga matasan hudu masu shekaru 2o zuwa 28.
Laftanar Oni, ya kara da cewa wadanda ake zargin suna cikin jerin wadanda aka jima ana nema ruwa a jallo saboda hannu kan garkuwa da mutane a Wukari da kewaye.
Babban Birget na 6, Birgediya Kingsley Chidebere Uwa, ya yaba wa sojojin saboda jajircewarsu wajen bin doka da oda.
Ya ce, jajircewarsu ce ta kai ga nasarar da aka samu.
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
