Labarai
Wasu masu neman dama ne suka ƙwace zanga-zangarmu – Matasan Nepal
Matasan Nepal da suka gudanar da zanga-zangar cin hanci da rashawa sun yi iƙirarin cewa wasu masu neman dama ne suka ƙwace zanga-zangar, suka rikiɗe ta zuwa tashin hankali da ɓarna yayin da sojojin Nepal suka fito sintiri a titunan Kathmandu, inda ƙasar mai tsaunuka ke fama da tashin hankali mafi muni cikin shekaru da dama.
Zanga-zangar da aka fara da nufin adawa da cin hanci da son kai ta rikiɗe a ranar Talata zuwa ƙone-kone da tashin hankali.
Firaministan ƙasar dai ya yi murabus bayan gidajen ’yan siyasa sun shiga hannun masu zanga-zangar tare da banka wa gine-ginen gwamnati wuta, har ma aka kutsa majalisar dokoki aka cinna mata wuta.
Ƙungiyoyin matasa sun nesanta kansu daga ɓarnar, suna masu cewa masu son yin amfani da dama ne suka shiga suka lalata zanga-zangar.
Sojoji sun kafa dokar hana fita a faɗin ƙasa har zuwa safiyar Alhamis, suna gargadin hukunta duk wanda aka samu da hannu a tashin hankali ko barna.
Rahotanni sun ce an kama mutum 27 da ake zargi da hannu a fashi da tarzoma, tare da ƙwato bindigogi 31.
Sojojin sun ce suna ƙoƙarin shawo kan lamarin da ke ƙara dagulewa, musamman bayan murabus ɗin Firaminista KP Sharma Oli ya haifar da giɓin shugabanci.
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
