Connect with us

Labarai

Tsofaffin Gwamnoni Sun Ziyarci Tinubu Tare Da Bashi Shawarwari Kan Matsalolin Tsaro

Published

on

Tsoffin gwamnoni da suka fara mulki a shekarar 1999, da ake kira “Class of ’99,” sun gana da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a Fadar Gwamnati da ke Abuja a ranar Juma’a, inda suka gabatar da shawarwari na aiki domin magance matsalolin tsaro, inganta tattalin arziki da kuma samar da ayyukan yi a fadin ƙasar.

Tawagar, ƙarƙashin jagorancin tsohon Gwamnan Jihar Edo, Lucky Igbinedion, ta haɗa da Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF), George Akume, da wasu tsoffin gwamnoni da suka yi mulki tare da Shugaba Tinubu lokacin da yake Gwamnan Jihar Lagos.

Da yake jawabi ga manema labarai bayan ganawar da ta ɗauki fiye da awa guda, Igbinedion ya bayyana cewa ziyarar tasu na da nufin yin wata ganawa da ɗan ajinsu kuma su tattauna hanyoyin da za a ciyar da ƙasa gaba.

Mun zo ganin takwaranmu, wanda muka fara mulki tare a shekarar 1999, don tattauna batutuwan da ke da muhimmancii ga ƙasa. Mun tattauna kan batun tsaro, tattalin arziki, noma da samar da ayyukan yi. Shugaban ya nuna damuwa matuƙa kan waɗannan matsaloli, kuma ya karɓi shawarwarinmu da hannu biyu.” In ji shi.

Igbinedion ya jaddada cewa tsaro ya kamata ya kasance babban fifiko na gwamnati, domin ba za a samu ci gaba ba tare da zaman lafiya idan ba tsaro ba.

Game da batun ayyukan yi, tsohon gwamnan ya yi kira da a kafa masana’antu kanana (cottage industries) a kowace ƙaramar hukuma a matsayin hanyar dorewar rage rashin aikin yi da fatara.

In har za ka ba mutum tallafi yau, me zai faru gobe? Mun roƙi Shugaban Ƙasa da ya kafa ƙanana masana’antu a faɗin ƙasa domin mutane su samu ayyukan yi.” In ji shi.

Tawagar ta yaba wa Shugaba Tinubu bisa maraba da shawarwari masu amfani, inda suka ce Shugaban Ƙasar ya tabbatar musu da cewa zai yi la’akari da duk wani tunani mai amfani da zai ciyar da ƙasa gaba.

Shugaban Ƙasa ya tabbatar mana cewa ƙofofinsa a bude suke don tattaunawa da shawarwari masu amfani da za su inganta ƙasar nan.” In ji Igbinedion.

Wannan shi ne karo na biyu da tsoffin gwamnoni na  1999 ke ziyartar Shugaban Ƙasa Tinubu tun bayan hawansa mulki.

 

Bello Wakili

 

Labarai

Labarai13 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara