Connect with us

Labarai

Tallafin Lafiya: Ƙungiyar Rotary Ta Raba Kayan Haihuwa kyauta Ga Mata Masu Juna Biyu  A Kaduna

Published

on

 

Ƙungiyar Rotary Club ta Kaduna Metropolitan ta raba kayan haihuwa fiye da 70 ga mata masu juna biyu a cibiyar kiwon lafiya ta Mando, Afaka.

 

Da yake jawabi a wajen taron, shugaban Rotary Club na Kaduna Metropolitan kuma shugaban Rotary Action Group for Peace, Rotarian Luqman Babatunde, ya jaddada cewa kayan haihuwar ba na siyarwa ba ne, kyauta ce don tallafa wa mata masu juna biyu musamman marasa ƙarfi.

 

Ya ce wannan tallafin ana gudanar da shi ne a wurare daban-daban a jihar Kaduna, yana mai jaddada cewa gwamnati kaɗai ba za ta iya yin komai ba, shi ya sa ake buƙatar goyon bayan ƙungiyoyin sa-kai da na taimakon jama’a irin su Rotary.

 

Ya bayyana cewa wannan shirin ya samu ne ta haɗin gwiwa da kamfanin MotherCat, wanda ke kusa da cibiyar lafiya, don tunawa da watan kula da lafiyar uwa da jarirai.

 

Ya shawarci matan da su yi amfani da kayan yadda ya kamata tare da tunatar da su taken Rotary, Service Above Self, yana mai ƙarfafa su su rika taimaka wa wasu idan dama ta samu.

 

Shi ma ya sake jan hankalin masu cin gajiyar su yi amfani da kayan cikin hikima.

 

Haka nan, gwamnan yankin Rotary Clubs, Rotarian Joy Okoro, wanda Rotarian Victor Majekodunmi ya wakilta, ya bayyana cewa mata da dama masu juna biyu waɗanda ba su da ƙarfin siyan kayan haihuwa kan haifi jarirai a gida cikin mawuyacin hali.

 

Ya jaddada cewa wannan kyauta ba ta gwamnati bace, an samo ta ne daga gudummawar kungiyoyi da mutane masu kishin jinƙai, yana mai roƙon matan su yi amfani da kayan yadda ya dace.

 

Ita kuma babban jinya ta cibiyar lafiya, Hajiya Murjanatu Ahmed Rabiu, ta koka kan yadda wasu mata masu juna biyu ke ɓoye kayan haihuwar da gwamnati ko kungiyoyin ci gaban al’umma suka ba su, domin su karɓi kuɗi daga mazajensu.

 

Ta yi gargadin cewa su daina wannan dabi’a, tana mai cewa an rubuta sunaye da lambobin wayar waɗanda suka amfana a yau, kuma idan ya zama dole za a sanar da mazajensu cewa matansu sun karɓi kayan haihuwa kyauta daga Rotary.

 

A sakon ta na musamman, shugabar Ƙungiyar Matan ‘Yan Jarida ta Najeriya (NAWOJ), Comrade Sahura Jibrin Maidoki, ta roƙi matan masu juna biyu su nuna kayan haihuwar ga mazajensu domin rage musu nauyin kuɗi da kuma bawa mazajen damar mayar da hankali kan wasu bukatu. Ta kuma yi gargadin cewa kada su sayar da magunguna da sauran kayan tsaftar da ke cikin kyautar.

 

Mata biyu da suka amfana, Salamatu Tijjani da Faith Tori, sun gode wa Rotary da abokan haɗin gwiwarta saboda kyautar, suka kuma yi alkawarin yin amfani da kayan yadda ya kamata.

 

Wasu daga cikin kayan da aka raba sun haɗa da magungunan mata masu juna biyu, jakunkuna, kayan tsafta, ‘pads’, da ‘diapers’ da sauransu.

 

Wannan shirin, wanda ya yi daidai da Watan Lafiyar Uwa da Jarirai na Rotary International, ya samu halartar shugaban Rotary Club na Kaduna Main, Rotarian Ahmad Tijjani, da sauran shugabannin ƙungiyar a Kaduna tare da abokan haɗin gwiwa ciki har da Mothercat da NAWOJ.

 

COV: Naomi Anzaku Ekele

 

Labarai

Labarai9 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara