Connect with us

Ilimi

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Published

on

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF), ta horas da malamai kan yadda za su gudanar da gwajin karatu da lissafi ga ɗaliban makarantun firamare.

Mai bada  shawara kan tantance ilimin yara a matakin farko na UNICEF Dakta Farouk Aliyu, ya bayyana cewa horon na kwanaki huɗu wanda ya fara a ranar Litinin, na da nufin tantance matsayin yadda dalibai ke koyon karatu a makarantu.

A cewarsa, sun mayar da hankali ne kan ɗaliban aji ɗaya da aji biyu na firamare da kuma malamansu a fannin lissafi da harshen Hausa a kowace makaranta.

Dakta Farouk Aliyu ya ce manufar wannan shiri ita ce samar da hanya mafi sauki da dalibai za su samu ƙwarewar karatu da lissafi a matakin farko a Jihar Jigawa.

Ya ƙara da cewa, ana kuma son fahimtar yadda malamai ke koyarwa tare da tantance ko suna bin hanyoyin koyarwa da UNICEF da sauran hukumomin ilimi suka koyar.

Ya ce idan aka samu gibi, hakan zai sa a sake horas da malamai da tsara manufofi, ko ma sauya tsarin manhajar karatu gaba ɗaya.

Mashawarcin na UNICEF ya ce an horas da mahalarta 67 waɗanda za su tattara sahihan bayanai masu inganci da za su taimaka wajen tsara manufofin da za su tallafa wa tsarin ilimi a jihar.

UNICEF ta dade tana tallafa wa tsarin ilimi a Jigawa da Najeriya baki ɗaya ta hanyar horas da malamai da samar da kayayyakin koyo da koyarwa.

Wannan horon ya ƙara jaddada ƙudirin Kungiyar Tarayyar Turai da gwamnatin Jihar Jigawa wajen inganta sakamakon koyo tare da tabbatar da cewa kowane yaro ya samu ƙwarewar karatu da lissafi tun daga tushe.

Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, an horas da sama da malamai 1,680 na azuzuwan firamare daya zuwa uku, kan hanyoyin koyar da karatu da lissafi  domin inganta koyarwa da samun sakamako mai kyau.

Haka kuma, an raba sama da kayayyakin koyo da koyarwa 152,386 ga ɗaliban matakin farko a makarantun da shirin ya shafa.

Labarai

Ilimi15 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara