Labarai
Sojojin Sun Kakkabe Wasu Manyan ‘Yan Bindiga A Zamfara
Rundunar sojojin Najeriya ta 1 karkashin jagorancin Birgediya Janar Timothy Opurum ta samu gagarumar nasara a yakin da take yi da ta’addanci da ‘yan bindiga a jihar Zamfara, musamman a kananan hukumomin Talata Mafara da Kaura Namoda.
A wata sanarwa da mukaddashin mataimakin daraktan hulda da jama’a na rundunar soji, Kyaftin Sulaiman Omale ya fitar tace a farkon farkon watan Mayun 2025, dakarun su da ke sintiri na yaki sun ci karo da dimbin ‘yan ta’adda da suka kutsa kai kauyen Mai Kwanugga a karamar hukumar Talata Mafara.
Ya yi bayanin cewa, ‘yan ta’addan sun rika kai hari kan mutanen yankin tare da kona gidaje kafin isowar sojojin, inda ya ce, bayan tuntubar rundunar, sojojin sun yi nasarar fatattakar ‘yan ta’addan bayan barin wuta, inda suka yi nasarar kashe ‘yan ta’adda da dama, ciki har da fitattun ‘yan ta’addan guda biyar da suka hada da Auta Jijji, Dankali, Sagidi, Kachallah Rijaji, da Kachallah Suza.
Sanarwar ta kuma ce, dakarun rundunar 1 sun bi sahun ‘yan ta’addan da suka tsere, inda aka samu nasarar kwato wasu tarin makamai da suka hada da bindigogi kirar AK-47 guda 4, Bindigan PKT 1, bututun RPG guda 2, bama-baman RPG guda 6, harsasai 28 na 7.62mm harsashi na musamman na PKT 3 da harsasai na musamman na PKT 3.
Birgediya Janar Timothy Opurum ya yabawa kwazon sojojin tare da tabbatar wa ‘yan kasar tabbacin da rundunar ta yi ba tare da bata lokaci ba na maido da zaman lafiya da tsaro a fadin jihar.
Rundunar sojin Najeriya ta karfafa gwiwar jama’a da su ci gaba da bayar da sahihin bayanai ga hukumomin tsaro tare da kaucewa daukar doka a hannunsu.
REL/AMINU DALHATU
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
