Labarai
Sojin Nijar Za Su Saki Bazoum
Gwamnatin mulkin soja a Jamhuriyar Nijar ta shiga sarkakiya bayan ta amince za ta saki hambararren shugaban kasar Mohamed Bazoum da matarsa Khadija.
Babban abin da ya jefa manyan jami’an soji a Jamhuriyar Nijar cikin rudani shi ne nacewar da Bazoum ya yi na ci gaba da zama a cikin kasar ta Nijar, bisa dalilin cewa ba ya sha’awar komawa wata kasa.
Wasu mazauna birnin Yamai, babban birnin kasar, da kuma Maradi daya daga cikin manyan biranen kasar, sun ce wata fitacciyar jarida a kasar cikin harshen Faransanci ta ambato labarin shirin sojojin na sakin Bazoum.
Majiyoyin sun ce hukumomin sojin na aiki kan yadda “abubuwa za su tafi daidai”, idan har suka bar Bazoum ya ci gaba da zama a Jamhuriyar Nijar.
Wani bangare na fargabar gwamnatin mulkin sojin shi ne yiwuwar samun zanga-zanga daga masu goyon bayan hambararren shugaban kasar domin neman a ba shi cikakken ‘yanci, tun da yarjejeniyar a halin yanzu ita ce Bazoum zai gaba da kasancewa a cikin wani tsari na daurin talalar zaman gida ba fita.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
