Connect with us

Kasuwanci

Shugaban Radiyon Najeriya Kaduna Ya Yi Babban Taron Farko Da Sashen Yada Labaran Gidan

Published

on

An gudanar da taron farko tare da sabon Daraktan Shiyya na Rediyon Najeriya Kaduna, a ranar Laraba, 10 ga Satumba, 2025.

 

Taron wanda aka fara shi da karfe 10 na safe, ya samu halartar dukkan ma’aikatan gudanarwa na sashen da sauran ma’aikatan.

 

Da yake jawabi ga ma’aikatan, Daraktan shiyya na FRCN Kaduna, Malam Haruna Idris ya bayyana fifikon sa ga labarai, inda ya jaddada cewa ba za a amince da sakaci a bakin aiki ba, sannan ya yi gargadi kan rashin da’a.

Ya nuna rashin jin dadinsa game da rashin tsaftar muhalli tare da yin kira da a sauya hali ta hanyar yin abin da ya dace.

 

Ya bayyana cewa kowa na da rawar da zai taka, don haka akwai bukatar a hada kai, ya kara da cewa ba zai lamunci munanan dabi’u ba.

 

Bugu da kari, Idris ya gargadi dukkan ma’aikata game da lokaci, yana mai nuni da cewa za a yi wa wadanda suke gaza cika alkawuran da suka dauka na zuwa aiki akan lokaci domin za a hukunta duk wanda ya aikata ba daidai ba

 

A cewarsa, ya shafe shekaru sama da ashirin da biyar yana aikin jarida, inda ya jaddada kudirinsa na sauya fasalin dakin labarai da ma Radio Nijeriya baki daya.

Malam Haruna Idris ya ba da umarnin cewa daga yanzu dole ne labarai su samar da ingantattun abubuwa na tsawon mintuna ashirin da biyar domin ci gaba da martabar gidan Rediyon Najeriya Kaduna.

 

Daraktan shiyyar ya shawarci ma’aikatan Labarai da al’amuran yau da kullum da su jajirce wajen gudanar da ayyukansu yadda ya kamata bisa ka’ida da ka’idojin aiki.

 

Idris ya sanar da cewa babban taron zai kasance duk wata, daga yanzu, ya kara da cewa halartar taron ya zama tilas ga kowane ma’aikaci kuma ya yi gargadin makararru.

“Idan na ce karfe 10 na safe, ina nufin karfe 10 na safe, don haka dole ne kowa ya kasance a kan lokaci a duk lokacin da na kira taro. A kan abubuwan da ke cikin labarai, a koyaushe ina sauraron labarai, saboda haka, dole ne kowa ya kasance da gaske ga abin da yake yi.

 

Tun da farko a jawabin bude taron mataimakin daraktan yada labarai (DDN) Aminu Abdullahi Gombi ya jaddada bukatar dukkan ma’aikatan su jajirce wajen gudanar da ayyukansu.

 

Ya koka akan mummunar dabi’ar nan ta rashin da’a tare da yin kira da a canza dabi’u, sannan ya bukace su da su tashi tsaye domin marawa Daraktan shiyya baya domin cimma burinsa na kawo sauyi a tashar.

 

Alhaji Haruna Idris ya kara jaddada aniyarsa ta magance kalubalen da Radio Nijeriya Kaduna ke fuskanta da yardar Allah, sannan ya nemi shawarwari masu kyau da za su ciyar da tashar gaba.

 

Sai dai ya yi alkawarin yin adalci ga kowa ba tare da la’akari da bambance-bambance ba.

 

Cov/ Sani Sulaiman

Labarai

Labarai4 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara