Labarai
Shugaban Hukumar Leken Asirin Isra’ila Ya Yi Murabus
Shugaban hukumar leken asiri ta kasar Isra’ila, Manjo-Janar Aharon Haliva, ya yi murabus saboda harin da ba a taba ganin irinsa ba da kungiyar Hamas ta kai wa kasar.
Manjo- Janar Aharon Haliva, shi ne babban hafsan soji na farko da ya yi murabus bayan caccakar da ya fuskanta kan gagarumin harin na ranar 7 ga watan Oktoban 2023.
A takardarsa ta barin aiki, Haliva ya ce ya dauki laifin kasa dakile harin da ya sa Hamas ta tsallaka katangar Iyaka da ma duk matakan tsaron Isra’ila har ta kai harin da aka kashe mutane dubu daya da dari daya da talatin da tara, ta kuma yi awon gaba da wasu darruruwa zuwa Gaza, inda ta yi garkuwa da su.
Ana ganin hakan zai bude kofa da manyan jami’an sojin kasar za su dauki laifin harin da ake ganin Hamas ta kada hantar Isra’ila fiye da kowane lokaci.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
