Connect with us

Labarai

Sanata Yari Ya Raba Shanu 380 Ga Al’umma Domin Bikin Sallah

Published

on

Sanata mai wakiltar mazabar Zamfara ta yamma, Alhaji Abdulaziz Yari Abubakar ya fara rabon shanu 380 ga mazabun siyasa 147 a kananan hukumomi 14 na jihar.

Da yake kaddamar da shirin rabon shanun da aka gudanar a Unguwar Kasuwar Daji da ke karamar Hukumar Kauran Namoda, shugaban kwamitin rabon Alhaji Lawal Liman Gabɗon Mattaura ya bayyana cewa, hakan na daga cikin karramawar Sanata Yari ga shuwagabanni da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC a jihar.

Lawal Liman wanda kuma shi ne shugaban kungiyar siyasar Sanatan ya ce kowace Unguwa za ta karbi shanu biyu domin gudanar da bukukuwan Sallah cikin farin ciki.

            Shugabannin kwamitin rabo

 

Shugaban wanda ya samu wakilcin dan kwamitin, Muhammad Muttaka Rini (Makaman Zamfara), ya bayyana cewa, Gundumomin da ke karkashin kananan hukumomi 4 da suka hada da Kaura Namoda, Zurmi, Shinkafi da Birnin Magaji da suka hada mazabar Sanatan Zamfara ta Arewa sun karbi kason su.

A cewarsa, sauran unguwannin kananan hukumomi 10 da ke karkashin mazabar Zamfara ta tsakiya da Zamfara ta yamma za su karbi nasu rabon ne tsakanin ranakun Litinin zuwa Talatar wannan makon.

A yayin da yake yabawa da irin namijin kokarin da Sanata Abdulaziz Yari Abubakar ya yi na yi wa al’ummarsa hidim, shugaban ya yi kira ga sauran shugabannin siyasar jihar da su yi koyi da irin wannan karamcin da nufin tabbatar da zaman lafiyar  al’umma da inganta  tattalin arzikin  don rage musu radadi.

Shugaban ya kuma yi kira ga al’ummar Musulmi musamman na jihar da wadanda suka je aikin Hajji da su yi amfani da wannan kwanaki goma na Zulhijja wajen karfafa addu’o’in samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar da kasa baki daya.

 

Sani Dutsinma

Labarai

Labarai13 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara