Labarai
Sanata Yari Ya Raba Shanu 380 Ga Al’umma Domin Bikin Sallah
Sanata mai wakiltar mazabar Zamfara ta yamma, Alhaji Abdulaziz Yari Abubakar ya fara rabon shanu 380 ga mazabun siyasa 147 a kananan hukumomi 14 na jihar.
Da yake kaddamar da shirin rabon shanun da aka gudanar a Unguwar Kasuwar Daji da ke karamar Hukumar Kauran Namoda, shugaban kwamitin rabon Alhaji Lawal Liman Gabɗon Mattaura ya bayyana cewa, hakan na daga cikin karramawar Sanata Yari ga shuwagabanni da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC a jihar.
Lawal Liman wanda kuma shi ne shugaban kungiyar siyasar Sanatan ya ce kowace Unguwa za ta karbi shanu biyu domin gudanar da bukukuwan Sallah cikin farin ciki.

Shugabannin kwamitin rabo
Shugaban wanda ya samu wakilcin dan kwamitin, Muhammad Muttaka Rini (Makaman Zamfara), ya bayyana cewa, Gundumomin da ke karkashin kananan hukumomi 4 da suka hada da Kaura Namoda, Zurmi, Shinkafi da Birnin Magaji da suka hada mazabar Sanatan Zamfara ta Arewa sun karbi kason su.
A cewarsa, sauran unguwannin kananan hukumomi 10 da ke karkashin mazabar Zamfara ta tsakiya da Zamfara ta yamma za su karbi nasu rabon ne tsakanin ranakun Litinin zuwa Talatar wannan makon.
A yayin da yake yabawa da irin namijin kokarin da Sanata Abdulaziz Yari Abubakar ya yi na yi wa al’ummarsa hidim, shugaban ya yi kira ga sauran shugabannin siyasar jihar da su yi koyi da irin wannan karamcin da nufin tabbatar da zaman lafiyar al’umma da inganta tattalin arzikin don rage musu radadi.
Shugaban ya kuma yi kira ga al’ummar Musulmi musamman na jihar da wadanda suka je aikin Hajji da su yi amfani da wannan kwanaki goma na Zulhijja wajen karfafa addu’o’in samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar da kasa baki daya.
Sani Dutsinma
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai13 hours agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
