Labarai
Sabon Sufeto Janar Ya Sha Alwashin Kawar da Cin Hanci da Rashawa a Tsakanin ‘Yan Sanda
Daga Bello Wakili
Sabon Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, Tunji Disu, ya bayyana godiyarsa ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, inda ya ce naɗin nasa ya zo masa a matsayin ba-zata.
Da yake magana jim kaɗan bayan bikin kaddamar da shi a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja, sabon shugaban ‘yan sandan ya gode wa Shugaban Ƙasa bisa amincewar da aka nuna masa.
Dangane da abubuwan da zai fara mayar da hankali a kai, Sufeto Janar ɗin ya ce zai fara da sake wayar da kan jami’ai da ma’aikata domin su fahimci cewa jama’a su ne ginshiƙin aikin ‘yan sanda.
Ya jaddada cewa babu wata rundunar ‘yan sanda a ko’ina cikin duniya da za ta yi nasara ba tare da haɗin kan jama’a ba, inda ya ƙara da cewa inganta walwalar jami’ai zai zama muhimmin mataki wajen ƙara ƙwazo da ƙwarewa a aiki.
Sufeto Janar ɗin ya sha alwashin kare haƙƙin ɗan Adam tare da ɗaukar matakin rashin haƙuri kan cin hanci da rashawa a tsakanin jami’an ‘yan sanda.
-
Labarai3 days agoAdalci a Kauru LGA Yayin da Tsarin Raba Mukamai ke Kara Karɓuwa Domin Wakilci Nagari
-
Labarai5 days agoHukumar Alhazan Jihar Jigawa ta Kaddamar da Kwamitin Amirul Hajjin Bana
-
Labarai2 days agoRadio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya
-
Labarai7 days agoTrump Ya Aike da Daftarin Shirin Zaman Lafiya ga Iran
-
Labarai2 days agoMasarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin
-
Labarai2 days agoHukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana
-
Labarai5 days agoHajjin2026: Jigawa ta Kara Kaimi Wajen Horar Da Maniyyata
-
Labarai2 days agoƊaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano
