Ilimi
Sabbin kwamishinonin Jihar Kano Bakwai da Ma’aikatunsu
Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf ya jagoranci rantsar da sabbin kwamishinoni bakwai da ya nada.
Kwamishinan shari’a na Kano Kuma babban lauyan jihar, Barista Haruna Isa Dederi ne ya rantsar da sabbin kwamishinonin tare da sauran masu ba Gwamna shawara.
Har ila yau dai Gwamnan ya jagoranci rantsar da sabbin manyan sakatarori Shida da aka daga likkafar su zuwa mataki a aikin Gwamnati da kuma rantsar da masu bashi shawara 13 daga cikin 15 da aka nada
Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf ya tura sabbin kwamishinonin zuwa ma’aikatun da aka tanadar musu.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya amince da tura su ma’aikatun da zasu jagoranta kamar haka.
Alhaji Shehu Wada Sagagi zai kula da ma’aikatar kasuwanci da zuba jari ta kano. Kwamared Ibrahim Abdullahi Waya, ma’aikatar kula da yada Labarai ta Kano. Sai Dakta Dahir Muhammad Hashim an amince ya rike ma’aikatar kula da Muhalli ta kano
Sauran su ne Abdulkadir Abdussalam, ma’aikatar kula da Raya karkara ta Kano. Dakta. Isma’ila Aliyu Dan Maraya, ma’aikatar kula da Kudi ta Kano. Dakta Gaddafi Sani Yakubu kuwa ma’aikatar Kula da makamashi ta Kano
Sai kuma Dakta.Nura Iro Ma’aji , ma’aikatar Kula da bada kwangiloli da bibiyar ayyukan gwamnati
Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya ce ya dauki matakin samar da sabbin kwamishinonin ne domin inganta ayyukan gwamnati da Kuma kawo ci gaba a Kano.
Abdullahi Jalaluddeen, Kano/Wababe
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
