Connect with us

Ilimi

Sabbin kwamishinonin Jihar Kano Bakwai da Ma’aikatunsu

Published

on

 

 

Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf ya jagoranci rantsar da sabbin kwamishinoni bakwai da ya nada.

 

Kwamishinan shari’a na Kano Kuma babban lauyan jihar, Barista Haruna Isa Dederi ne ya rantsar da sabbin kwamishinonin tare da sauran masu ba Gwamna shawara.

 

Har ila yau dai Gwamnan ya jagoranci rantsar da sabbin manyan sakatarori Shida da aka daga likkafar su zuwa mataki a aikin Gwamnati da kuma rantsar da masu bashi shawara 13 daga cikin 15 da aka nada

 

Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf ya tura sabbin kwamishinonin zuwa ma’aikatun da aka tanadar musu.

 

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya amince da tura su ma’aikatun da zasu jagoranta kamar haka.

 

Alhaji Shehu Wada Sagagi zai kula da ma’aikatar kasuwanci da zuba jari ta kano. Kwamared Ibrahim Abdullahi Waya, ma’aikatar kula da yada Labarai ta Kano. Sai Dakta Dahir Muhammad Hashim an amince ya rike ma’aikatar kula da Muhalli ta kano

 

Sauran su ne Abdulkadir Abdussalam, ma’aikatar kula da Raya karkara ta Kano. Dakta. Isma’ila Aliyu Dan Maraya, ma’aikatar kula da Kudi ta Kano. Dakta Gaddafi Sani Yakubu kuwa ma’aikatar Kula da makamashi ta Kano

 

Sai kuma Dakta.Nura Iro Ma’aji , ma’aikatar Kula da bada kwangiloli da bibiyar ayyukan gwamnati

 

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya ce ya dauki matakin samar da sabbin kwamishinonin ne domin inganta ayyukan gwamnati da Kuma kawo ci gaba a Kano.

Abdullahi Jalaluddeen, Kano/Wababe

Labarai

Labarai9 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara