Labarai
Rundunar Operation Fansan Yamma Ta Raba Takin Zamani Ga Monoma A Karamar Hukumar Tsafe
A wani yunkuri na kokarin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Arewa maso Yamma da wasu sassan Arewa ta Tsakiya, Kwamandan Rundunar Operation Fansan Yamma, Manjo Janar O.O. Soyele, ya raba buhunan taki 200 ga manoma a karamar hukumar Tsafe ta Jihar Zamfara.
Wata sanarwa da jami’in yada labarai na rundunar Kyaftin David Adewusi, ya fitar ta bayyana cewa wannan tallafi an yi shi ne da nufin karfafa amfanin gona da inganta rayuwar al’umma a yankin.

Janar Soyele wanda ya sami wakilcin Kwamandan Sashen Kayayyakin Aiki na Rundunar, Birgediya Janar Nkemakolam Mbaka, ya mika buhunan takin ga Sarkin Tsafe, Alhaji Abubakar Muhammad Bawa, a matsayin wani bangare na shirin kyautata hulɗa tsakanin sojoji da al’umma, na Hedikwatar Tsaro.

Janar Soyele ya bayyana cewa wannan shiri na hanyar sulhu ba tare da amfani da karfi ba an yi shi ne domin bunkasa harkar noma, karfafa hulɗar sojoji da al’umma, da kuma ƙarfafa manoma su koma gona, a daidai lokacin da ake gudanar da samamen kawar da barazanar tsaro a yankunan noma.

Kwamandan ya kuma gode wa Sarkin Tsafe, gwamnati da al’ummar Jihar Zamfara bisa goyon bayan da suke bayarwa wajen yaki da ta’addanci da ’yan bindiga.
Ya shawarci manoma da su yi amfani da takin yadda ya kamata domin samun karin amfanin gona.

A nasa jawabin, Sarkin Tsafe, Alhaji Abubakar Muhammad Bawa, ya gode wa Kwamandan Rundunar bisa abin da ya bayyana a matsayin taimakon da ya zo a kan gaba. Ya ce wannan kyauta za ta inganta samar da abinci da kuma kyautata rayuwar manoma, tare da tabbatar da ci gaba da goyon baya ga sojoji.

Taron ya samu halartar shugabannin al’umma, wakilan shugaban karamar hukumar Tsafe, da kuma jama’ar garin da suka yaba da wannan shiri.
Daga Aminu Dalhatu
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
