Labarai
PDP ta Sallami Wike, Fayose, Anyanwu da Wasu Mutane
Jam’iyyar PDP ta kori Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, tsohon gwamnan Jihar Ekiti, Ayodele Fayose da tsohon sakataren jam’iyyar na ƙasa, Samuel Anyanwu.
PDP ta yanke wannan hukunci ne a babban taron jam’iyyar da ake gudanarwa a Ibadan, babban birnin Jihar Oyo.
Tsohon Mataimakin Shugaban Jam’iyyar na yankin Kudu, Cif Olabode George ne, ya gabatar da ƙudirin korarsu, sannan Samaila Burga, shugaban PDP na Jihar Bauchi, ya mara masa baya.
A baya, bangaren jam’iyyar da ke goyon bayan Wike sun kai ƙara kotu don a hana gudanar da taron.
Amma PDP ta samu hukuncin da ya ba ta damar ci gaba da taron daga Kotun Ƙoli ta Jihar Oyo.
Kwana biyu kafin taron, Mao Ohuabunwa, Shugaban Majalisar Amintattu (BoT) na ɓangaren Wike, ya ce duk wanda ya tafi Ibadan don taron hutu ya je yi, domin doka ba za ta aminta da shi ba.
A cewarsa, Anyanwu ya riga ya fitar da sanarwar ɗage taron.
Ohuabunwa ya ce: “Mun zauna a matsayin kwamitin zartarwa na ƙasa na PDP, muka duba abubuwan da muka yi. Mun yadda da bin hukuncin kotu game da taron Ibadan. Don haka ba mu da hannu a taron.
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
