Connect with us

Labarai

NIPR Ta Bai Wa Gwamnan Jigawa Lambar Yabo Ta Musamman Bisa Samar Da Abinci Ga Kasa

Published

on

Gwamna Umar Namadi na jihar Jigawa ya yi alkawarin aiwatar da wasu tsare-tsare da za su bunkasa noma da sauran abubuwan da suka shafi bunkasa noma a jihar.

Ya bayyana haka ne a Dutse a wani gagarumin biki da Cibiyar Koyar da Dabarun Yada Labarai da Hulda da Jama’a ta Kasa NIPR ta shirya, inda ta ba shi lambar yabo ta musamman a fannin samar da abinci.

Gwamna Umar Namadi ya bayyana cewa daya daga cikin dabarun ci gaban gwamnatin jihar shi ne tabbatar da dorewar aikin noma da nufin samar da ayyukan yi a jihar.

Gwamna Namadi ya yi nuni da cewa, fifikon da gwamnatin jihar ta bai wa noma shi ya sa jihar ta kasance kan gaba wajen samar da wasu kayan abinci da kudi a kasar nan da suka hada da alkama, shinkafa, ridi da ganyen zobarodo.

Ya ce, wannan kokarin ya kuma sanya jihar ta zamto kan gaba a fannin bayar da gudunmawa wajen samar da abinci ga kasa da habbaka tattalin arzikin kasa.

 

Ya bayyana cewa bunkasa fannin noma ya yi daidai da burin ci gaba mai dorewa na kawo karshen yunwa, da samar da wadataccen abinci da inganta abinci mai gina jiki da kuma bunkasa noma mai dorewa.

Namadi ya godewa NIPR bisa wannan karramawar sannan ya yi alkawarin bullo da wasu tsare-tsare da za su kawo sauyi a fannin noma a jihar.

Tun da farko a nasa jawabin, shugaban NIPR Dakta Ike Neliaku, ya ce lambar yabo ta NIPR na da nufin karfafa kyakkyawan shugabanci a matakai daban-daban na gwamnati.

Ya kuma yabawa gwamnan kan wasu tsare-tsare da suka karfafa samar da abinci wanda kuma ya samar da ayyukan yi ga dubban jama’a tare da bunkasa darajar aikin gona.

A halin da ake ciki, kwamishinan yada labarai, da kwamishinan Kudi, da na kananan hukumomi na jihar Jigawa sun yi jawabai daban daban kan tasirin aikin sauya fasalin noma na jihar Jigawa ga harkokin tsaro da sauran bangarori daban daban na jihar.

Gidan Rediyon Najeriya  ya ruwaito cewa, an bai wa Gwamna Umar Namadi  matsayin Uban cibiyar ta  NIPR reshen jihar Jigawa.

 

Usman Muhammad Zaria

Labarai

Labarai10 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara