Fasaha
Mutane 3 Sun Mutu a Salga a Kano

Mazauna kauyen Yar’Gwanda dake karamar hukumar Tsanyawa ta Kano suna zaman jimami sakamakon rasuwar wani tsoho mai shekaru 60 mai suna Malam Danjuma da dansa Ibrahim mai shekaru 35 da haihuwa da kuma abokinsa Aminu Gaye da suka mutu a salga ko makewayi a kokarin cire wata wayar salula da ta fada a Masai irin na gargajioyar nan.
Jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar Kano Saminu Yusif Abdullahi ya tabbatar da faruwar lamarin.
Ya bayyana cewa hukumar ta samu kiran gaggawa daga tashar kashe gobara ta Tsanyawa cewa wasu mutane hudu sun makale a a salga ko masai na gargajiya a lokacin da suke kokarin dauko wayar salular da ta fada.
Ya kuma jaddada cewa, nan take aka tura tawagar ceto zuwa wurin inda aka gano cewa Danjuma ya yi kokarin dauko wayarsa da ta fada cikin bandakin, inda ya makale. Bayan haka, dansa ya shiga bandaki don ya ceci mahaifinsa shi ma shiru sai abokinasa Gaye da Alasan suma sun shiga ne domin ceto mutanen biyu kuma suma suka makale.”
Saminu ya bayyana cewa, an ceto mutanen 3 na farko a sume yayin da na hudun na raye.
Jami’in hulda da jama’a ya ce rundunar ‘yan sandan ta kai wadanda lamarin ya rutsa da su zuwa asibitin musamman na Bichi inda likitocin da ke bakin aiki suka tabbatar da mutuwar mutane ukun yayin da na hudun mai suna Abba Alhassan mai shekaru 28 a duniya yana samun kulawar likitoci.
Ya ce an mika wadanda suka mutun ne ga baturen ‘yansandan Tsanyawa Iro Lado.
Saminu ya bukaci jama’a da su daina jefa kansu cikin hadari, ya kuma shawarce su da su kai rahoton faruwar gobara, nutsewa, rugujewar gine-gine, da hadurran mota da dai sauransu zuwa ofishin hukumar kashe gobara mafi kusa da su ko kuma ta lambobin wayarsu na dake aiki ba dare ba rana.
KHADIJAH ALIYU/Wababe
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
