Connect with us

Kasuwanci

Minista Matawalle ya Karɓi Manyan Jiga-Jigan PDP Da Suka Koma Jam’iyyar APC

Published

on

Aƙalla shugabanni 15 na jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) a Jihar Zamfara sun sauya sheka zuwa All Progressives Congress (APC).

 

An gabatar da waɗannan waɗanda suka sauya shekar ne a gaban Ministan Harkokin Tsaro na Ƙasa, Dr. Bello Mohammed Matawalle, a Abuja ranar Laraba, ta hannun Shugaban APC na Jihar Zamfara, Alhaji Tukur Umar Danfulani, tare da Sanata Tijjani Yahaya Kaura da Alhaji Lawal M. Liman.

 

A cewar wata sanarwa da Mai Magana da yawun jam’iyyar APC na Jihar Zamfara, Yusuf Idris Gusau, ya fitar, Minista Matawalle ya tarbi sabbin ’yan jam’iyyar da farin ciki, inda ya tabbatar musu da daidaito da damar ci gaba da aiki a cikin jam’iyyar.

 

Dr. Matawalle ya bayyana matakin da suka ɗauka na komawa APC a matsayin abin jarumtaka kuma daidai da lokaci, tare da nuna farin ciki kan yadda jam’iyyar ke ƙara samun karɓuwa a Zamfara da ma ƙasa baki ɗaya.

 

Ya yaba wa shugabannin jam’iyyar a matakin jiha bisa jajircewar su wajen tuntuba da wayar da kan jama’a, wanda ya ce hakan ya ƙarfafa martabar APC a sassan jihar.

 

Da yake gabatar da waɗanda suka sauya sheka, Shugaban APC na Jihar Zamfara, Tukur Umar Danfulani, ya bayyana cewa sabbin ’yan jam’iyyar sun haɗa da manyan shugabanni 15 na PDP a matakin jiha da yankuna, waɗanda suka shiga APC domin shirye-shiryen zaɓen 2027.

 

Ya ce an karɓe su tun da farko ta hannun Sanata Tijjani Yahaya Kaura, a madadin tsohon Gwamnan Jihar Zamfara kuma Sanata mai wakiltar Zamfara ta Yamma, Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar.

 

 

Daga cikin fitattun waɗanda suka sauya sheka akwai: Isiyaka M. Dabo, Shugaban Matasa na PDP; Nasiru Mohammed Anka, Ma’ajin Yankin Zamfara ta Yamma; Junaidu Magaji Kiyawa, Sakataren Shirye-shirye na PDP na Zamfara ta Arewa; Musa Halilu Faru, Mataimakin Sakataren Shirye-shirye na Zamfara ta Yamma; Alhaji Lawali Aliyu Shinkafi, Sakataren Yanki na Zamfara ta Arewa; da kuma Hajiya Rabi Bakura da Hajiya Amina Duniya, waɗanda duka Ex-Officio ne na PDP a matakin jiha.

 

Sauran sun haɗa da Bashar Mohammed Dogon Kade, tsohon ɗan takarar majalisar jiha ta Kaura Namoda South, da Rilwanu Bello, tsohon ɗan takarar kansila.

 

Shi ma Sanata Tijjani Kaura, ya bayyana wannan sauya sheka a matsayin babban abin farin ciki ga APC, yana mai cewa sabbin mambobin za su ƙara ƙarfafa ginin jam’iyyar da kyautata damar ta a gaban zaɓen 2027.

 

Ita kuwa Hajiya Amina Duniya, wacce ta ce ta shafe shekaru 25 a jam’iyyar PDP, ta yi alkawarin jawo ƙarin magoya baya zuwa APC tare da kira da a tabbatar da adalci da daidaito ga kowa.

 

Taron ya samu halartar manyan jiga-jigan APC da suka haɗa da: Hon. Lawal M. Gabdon Kaura, tsohon shugaban APC; Alhaji Kabiru Balarabe, tsohon Sakataren Gwamnati; Hon. Yazid Shehu Danfulani, Manajan Darakta na NIAC; Barr. Aminu Junaidu, tsohon Kwamishinan Shari’a; Alhaji Sha’ayau Yusuf Talata-Mafara; Hon. Ibrahim Maigandi Danmalikin Gidan Goga, mai ba Minista shawara kan harkokin siyasa; da Malam Yusuf Idris Gusau, Mai Magana da yawun jam’iyyar, da sauransu.

 

Aminu Dalhatu

Labarai

Labarai4 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara