Connect with us

Labarai

Max Air Zai Yi Jigilar Alhazan Jigawa A Ranakun 20 Da 21 Ga Watan Mayu

Published

on

A kokarin da yake yi na jigilar maniyyatan aikin hajjin bana, Kamfanin jiragen sama na Max Air yace zai kwashe daukacin Alhazan Jihar Jigawa cikin kwanaki biyu.

 

Mataimakin mai kula da ofishin kamfanin dake jihar kano, Mr Barnabas Anderson ya bayyana haka a lokacin taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a shelkwatar hukumar Jin dadin alhazan jihar Jigawa dake Dutse babban birnin jihar.

A cewarsa, ana sa fara jigilar maniyatan jihar  zuwa kasar Saudi Arabia a ranar 20 da kuma 21 ga watan Mayun 2025.

 

Ya ce jirgin Max air zai yi sawun farko da maniyata su 550 zuwa kasa mai tsarki a ranar 20 ga watan Mayu.

 

Mr Anderson yace a ranar 21 kuma, jirgi na biyu zai dauki maniyata 400 zuwa kasar Saudi Arabia.

Yayi nuni da cewar,jami’an kamfanin za su iso Dutse a ranar 19 ga wata domin kammala duk wani shiri na jigilar maniyatan.

 

Ya kuma ce kamfanin max air zai tabbatar da ganin an yi jigilar maniyatan cikin kwanciyar hankali domin sauke nauyin da aka dora masa.

 

Shi ma a nasa jawabin, wakilin hukumar aikin hajji ta kasa mai kula da jihohin Kano da Jigawa, Alhaji Salisu Gaya ya ce hukumar za ta tabbatar da ganin an yi jigilar maniyatan Jihar Jigawa cikin tsari.

A don haka, ya kuma bukaci maniyyatan da su kiyaye da ka’idoji da kuma dokokin kasa mai tsarki domin kare kima da kuma martabar kasa Najeriya.

 

A jawabinsa, Darakta Janar na hukumar Jin dadin alhazan jihar jigawa, Alhaji Ahmed Umar Labbo yace hukumar ta raba dukkannin kayayyakin aikin hajji ga maniyyata ta hannun shugabannin shiyya-shiyya na hukumar.

 

Ya kara da cewar, hukumar ta kuma kammala aiki akan takardun biza na maniyyata da yi musu allurar rigakafi da kuma tanadin kudaden guzuri wato BTA.

Alhaji Ahmed Umar Labbo yace makasudin gudanar da taron masu ruwa da tsakin shi ne, domin bibiyar shirye-shiryen da suka yi na samun nasarar aikin hajjin bana dake tafe.

 

Labbo, ya kuma bayyana cewar, hukumar ta biya bashin naira miliyan dubu 3 da miliyan 360 da Gwamnatin jihar ta bata rance domin sayen kujerun aikin hajjin bana.

 

Ya Kara da cewar, rancen kudin ya  matukar taimakawa hukumar wajen tare kujerun maniyyatan jihar a hukumar aikin hajji ta kasa wato NAHCON.

 

Kazalika, ya yabawa Gwamna Umar Namadi bisa hadin kai da goyon bayan da yake baiwa hukumar a kowanne lokaci.

 

 

Usman Mohammed Zaria

Labarai

Labarai9 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara