Labarai
Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin
Daga Yusuf Zubairu
Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere da su rungumi hadin kai da fahimtar juna domin samar da zaman lafiya da ci gaba mai dorewa.
Sarkin Saminaka, Alhaji Musa Sani Ibrahim, ya yi wannan kira a fadarsa yayin ziyarar gaisuwar Sallah da masu rike da sarautun gargajiya suka kai masa a lokacin bikin Eid al-Fitr.
Sarkin ya bukaci mazauna yankin da su ci gaba da rayuwa cikin zaman lafiya da jituwa ba tare da la’akari da bambancin kabila ko addini ba, yana mai jaddada cewa hadin kai shi ne ginshikin ci gaba.
Har ila yau, ya yi kira ga gwamnatoci a dukkan matakai da su kara kaimi wajen samar da kayan aikin noma da kuma magance matsalar tsaro, domin bai wa manoma damar gudanar da ayyukansu cikin sauki, wanda hakan zai taimaka wajen tabbatar da wadatar abinci.
Yayin da yake gode wa masu rike da sarautun gargajiya bisa goyon baya da biyayya da suke nuna wa masarautar, Sarkin ya bukace su da su ci gaba da zama jakadu nagari tare da mara wa gwamnati mai ci baya domin tabbatar da zaman lafiya da ci gaba.
A nasa jawabin, Egwe na al’ummar Igbo a Saminaka, Mista John Eze, ya nuna godiya ga majalisar masarautar bisa shugabanci mai hada kai da adalci.
Mista Eze ya yabawa salon jagorancin Sarkin, tare da jaddada kudirin al’ummar Igbo na bada gudunmawarsu wajen ci gaban yankin.
Shi ma da yake jawabi, Tafarkin Saminaka, Alhaji Musa Suleiman Tanko, ya bayyana masarautar a matsayin daya daga cikin mafi zaman lafiya a Jihar Kaduna, tare da tabbatar da cewa sarakunan gargajiya za su ci gaba da aiki tukuru domin dorewar zaman lafiyar da ake da shi domin amfanin kowa.
-
Labarai3 days agoAdalci a Kauru LGA Yayin da Tsarin Raba Mukamai ke Kara Karɓuwa Domin Wakilci Nagari
-
Labarai5 days agoHukumar Alhazan Jihar Jigawa ta Kaddamar da Kwamitin Amirul Hajjin Bana
-
Labarai2 days agoRadio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya
-
Labarai7 days agoTrump Ya Aike da Daftarin Shirin Zaman Lafiya ga Iran
-
Labarai7 days agoGwamnatin Kano ta Samar da Babura Don Inganta Yaki da Cutar Tarin Fuka a Karkara
-
Labarai7 days agoKebbi: An Samu Asarar Rayuka a Rikicin Alwasa
-
Labarai5 days agoHajjin2026: Jigawa ta Kara Kaimi Wajen Horar Da Maniyyata
-
Labarai2 days agoHukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana
