Ilimi
Malamai Na Karbar Horo Akan Shirin Ilimin Mata Na AGILE a Jigawa
Shirin karfafa karatun mat (AGILE), ya fara horar da Malamai 60 na kwanaki 3 domin gudanar da shirin ba da ilimi na zamani mai suna dama ta biyu ta samun ilimi. “Second chance education bangaren” a Kano.
Shugabar Bangaren Aikin, Miss Hafsat Adhama, ta bayyana haka a wajen taron cin abincin rana da aka gudanar a Dutse, babban birnin jihar Jigawa.
Ta bayyana cewa, sama da malamai 300 ne suka gabatar da aikace-aikacen kuma an tantance su bisa la’akari da cancantarsu, da gogewa a fannin ilimin boko, fahimtar yanayin gida, da kuma sha’awar yara mata masu tasowa.
Ta yi nuni da cewa, tsarin ya ƙare ne a zaɓin ƙwararrun malamai 60, tare da tabbatar da cewa an zaɓi mafi kyawun kayan aiki da ma’aikata ne kawai don tallafawa shirin AGILE.
Miss Hafsat Adhama ta ce, wannan tsattsauran tsarin zaɓen, yana ƙara jaddada himmar shirin AGILE da abokan haɗin gwiwarsa, na samarwa ‘yan mata ilimi dama na biyu mai ma’ana don samun kyakkyawar makoma.
Ta kuma bayyana cewa, kimanin cibiyoyin koyo 60 ne aikin ya gano a wurare daban-daban a fadin kananan hukumomi 44 na jihar Kano. Don haka Hafsat ta umurci wadanda suka ci gajiyar shirin da su mai da hankali a lokutan horon
A nasa jawabin, mai ba da shawara kan harkokin fasaha na shirin Farfesa Auwal Halilu ya jaddada muhimmancin wannan horon, inda ya ce horo ne na musamman da ke bukatar maida hankali.
Ya kuma bukaci mahalarta taron da su kula domin akwai gibi mai yawa tsakanin ilimin boko.
Farfesa Halilu ya bukace su da su kasance masu sada zumunci da saukin kai, domin sanya ilimin da ake bukata a cikin zukatan daliban.
A yayin gabatar da nasa jawabin, kodinetan aikin, Alhaji Mujittapha Aminu ya ce, tantance cibiyoyin koyo ya ba da fifiko wajen samun dama, aminci da taimakon al’umma.
A cewarsa, samar da ababen more rayuwa don samar da yanayi mai kyau da kwanciyar hankali ga ‘yan mata masu tasowa, su ma abubuwan da aka yi la’akari da su wajen zabar wuraren koyo.
Ya kara da cewa, an gano sama da cibiyoyin koyo 100 a fadin kananan hukumomi 44, amma duk da haka an kammala tantance cibiyoyin koyo guda 20.
Alhaji Mujttapha ya jaddada cewa, za su tabbatar da cewa an zabo ma’aikata masu inganci don tallafawa shirin AGILE.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, Shirin Koyar da ’Yan Matan Matasa (AGILE) da ke Kano, wani muhimmin shiri ne da aka tsara don samarwa ‘yan mata masu tasowa damar samun ingantaccen ilimi na biyu ta hanyar guraben karatu na yau da kullun.
Shirin yana da nufin cike gibin ilimi ga ‘yan matan da ba sa zuwa makaranta, inganta daidaiton jinsi da karfafawa ‘yan mata matasa ilimi da dabarun rayuwa masu mahimmanci don ci gaban kansu da zamantakewa.
USMAN MZ
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
