Connect with us

Labarai

Ma’aikatan Lafiya na BKD-HEALTH Sun Karrama Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Ma’aikatan lafiya na BKD-HEALTH sun karrama shugaban karamar hukumar Birnin Kudu, Dr. Builder Muhammad Uba, bisa shugabanci nagari da kuma daukar matasa aiki.

A jawabinsa na maraba, jagoran ma’aikatan na BKD-HEALTH Nasiru Sanusi ya ce taron ya dace da cikar su shekara daya da samun wannan aiki wanda ma’aikata 210 ke samun alawus ba tare da yankewa ba.

A sakonsa na fatan alkairi, shugaban sashen kula da tsaftar ruwa da muhalli na karamar hukumar ta bakin Malam Saminu Musa, ya ce baya ga daukar ma’aikatan BKD-HEALTH domin inganta aikin lafiya, shugaban karamar hukumar yana kashe naira milyan 5 duk wata wajen tallafawa marasa lafiya da kudaden magani.

Shi ma a nasa jawabin, Kansilan ayyuka Alhaji Haladu Maigari, ya ce cikin watanni da kama mulkinsa, shugaban karamar hukumar ya gyara asibitoci guda 7.

Ya kuma jinjinawa ma’aikatan na BKD-HEALTH bisa lura da kokarin shugaban karamar hukumar, inda ya yi addu’ar nan gaba za a ba su aiki na dindindin.

Wasu daga cikin ma’aikatan na BKD-HEALTH Sulaiman Yusuf, Ai’sha Isma’il Sulaiman da Ummu Salma Abdullahi sun ce sun kwashe shekara da shekaru a matakin aikin sa kai da na wucin gadi.

 

Sun kuma godewa shugaban karamar hukumar bisa samun wannan dama.

Da ya ke mayar da jawabi, shugaban karamar hukumar Birnin Kudu, Dr. Builder Muhammad Uba ya bukaci ma’aikatan na BKD-HEALTH da su rike ayyukan su bisa gaskiya da Amana domin kuwa karin alawus din su zai dogara akan kwazo da mutunta aiki.

Ya bayyana taron a matsayin cikakkiyar sheda kan abubuwan da ke wakana a karamar hukumar Birnin Kudu.

Builder, ya yi kira ga jama’ar yankin da su shiga a dama da su wajen yankar katin zabe da na jam’iyar APC domin ciban yankin.

Sauran wadanda aka karrama tare da shugaban karamar hukumar sun hadar da Alhaji Haladu Maigari da Alhaji Ibrahim Isyaku da Malam Muhammad Musa Badamasi da Mai kula da shirin BKD-HEALTH, Mujittafa Ibrahim.

 

Labarai

Ilimi15 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara