Labarai
Ma’aikatan Lafiya na BKD-HEALTH Sun Karrama Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu
Daga Usman Muhammad Zaria
Ma’aikatan lafiya na BKD-HEALTH sun karrama shugaban karamar hukumar Birnin Kudu, Dr. Builder Muhammad Uba, bisa shugabanci nagari da kuma daukar matasa aiki.
A jawabinsa na maraba, jagoran ma’aikatan na BKD-HEALTH Nasiru Sanusi ya ce taron ya dace da cikar su shekara daya da samun wannan aiki wanda ma’aikata 210 ke samun alawus ba tare da yankewa ba.

A sakonsa na fatan alkairi, shugaban sashen kula da tsaftar ruwa da muhalli na karamar hukumar ta bakin Malam Saminu Musa, ya ce baya ga daukar ma’aikatan BKD-HEALTH domin inganta aikin lafiya, shugaban karamar hukumar yana kashe naira milyan 5 duk wata wajen tallafawa marasa lafiya da kudaden magani.
Shi ma a nasa jawabin, Kansilan ayyuka Alhaji Haladu Maigari, ya ce cikin watanni da kama mulkinsa, shugaban karamar hukumar ya gyara asibitoci guda 7.

Ya kuma jinjinawa ma’aikatan na BKD-HEALTH bisa lura da kokarin shugaban karamar hukumar, inda ya yi addu’ar nan gaba za a ba su aiki na dindindin.
Wasu daga cikin ma’aikatan na BKD-HEALTH Sulaiman Yusuf, Ai’sha Isma’il Sulaiman da Ummu Salma Abdullahi sun ce sun kwashe shekara da shekaru a matakin aikin sa kai da na wucin gadi.
Sun kuma godewa shugaban karamar hukumar bisa samun wannan dama.
Da ya ke mayar da jawabi, shugaban karamar hukumar Birnin Kudu, Dr. Builder Muhammad Uba ya bukaci ma’aikatan na BKD-HEALTH da su rike ayyukan su bisa gaskiya da Amana domin kuwa karin alawus din su zai dogara akan kwazo da mutunta aiki.
Ya bayyana taron a matsayin cikakkiyar sheda kan abubuwan da ke wakana a karamar hukumar Birnin Kudu.

Builder, ya yi kira ga jama’ar yankin da su shiga a dama da su wajen yankar katin zabe da na jam’iyar APC domin ciban yankin.
Sauran wadanda aka karrama tare da shugaban karamar hukumar sun hadar da Alhaji Haladu Maigari da Alhaji Ibrahim Isyaku da Malam Muhammad Musa Badamasi da Mai kula da shirin BKD-HEALTH, Mujittafa Ibrahim.
-
Labarai3 days agoAdalci a Kauru LGA Yayin da Tsarin Raba Mukamai ke Kara Karɓuwa Domin Wakilci Nagari
-
Labarai5 days agoHukumar Alhazan Jihar Jigawa ta Kaddamar da Kwamitin Amirul Hajjin Bana
-
Labarai2 days agoRadio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya
-
Labarai7 days agoTrump Ya Aike da Daftarin Shirin Zaman Lafiya ga Iran
-
Labarai2 days agoMasarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin
-
Labarai2 days agoHukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana
-
Labarai5 days agoHajjin2026: Jigawa ta Kara Kaimi Wajen Horar Da Maniyyata
-
Labarai2 days agoƊaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano
