Connect with us

Labarai

Kotu Ta Bada Belin Tsohon Gwamnan Jihar Kwara

Published

on

Wata babbar kotun tarayya da ke Ilorin babban birnin jihar Kwara, ta bayar da belin tsohon gwamnan jihar, Alhaji Abdulfatah Ahmed a kan kudi naira miliyan hamsin, bisa zargin almubazzaranci da kudade a lokacin da yake mulki daga shekarar 2011 zuwa 2019.

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC na tuhumar Abdulfatah bisa zargin almubazzaranci da kudaden jama’a har Naira Miliyan Dubu Daya .

Tsohon gwamnan, wanda ya kai kansa zuwa ofishin hukumar EFCC shiyyar Ilorin a ranar Litinin 19 ga watan Fabrairun 2024, an tsare shi ne bisa wasu sharuddan beli.

A hukuncin da ta yanke bayan sauraron bangarorin biyu, Mai shari’a Evelyn Anyadike ta bayar da sharuddan beli guda takwas domin sakin tsohon gwamnan.

 

Mai shari’a Anyadike ta ce sharuddan belin sun hada da Naira miliyan 50 , da mutum biyu da za su tsaya masa da kadarorinsu a garin Ilorin da kuma mika fasfo dinsa na tafiye-tafiye zuwa kasashen waje ga magatakardar kotun, da dai sauransu.

Da yake amsa tambayoyi daga manema labarai, lauyan hukumar EFCC Rotimi Jacobs (SAN) wanda ya bayyana cewa wanda ake kara yana kan shari’a da tuhume-tuhume 12, ya kuma ki amsa laifinsa a lokacin da aka karanta masa tuhume-tuhumen.

A nasa tsokacin, lauyan wanda ake kara, Kehinde Eleja (SAN), ya koka da yadda ake musgunawa wanda yake karewa.

An dage ci gaba da sauraron karar zuwa ranakun 29 da 30 ga watan Afrilu na wannan shekara ci gaba da domin sauraren karar

Ali Muhammad Rabi’u

Labarai

Labarai4 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara