Connect with us

Labarai

Kasafin Kudin Bana Zai Samarda Tsarin Tattalin Arziki Da Cigaban Ƙasa: Ministan Labarai

Published

on

 

Ministan Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Mohammed Idris, ya bayyana kasafin kuɗin bana, wanda Shugaba Tinubu ya rattaba wa hannu kwanan nan, a matsayin tsari mai karfi da zai daidaita tattalin arziki da kwanciyar hankali a zamantakewa, da kuma cigaban ƙasa.

 

Ya bayyana hakan ne a yayin taron da ake da Ministoci karo na uku da aka gudanar a Cibiyar Manema Labarai ta Ƙasa, Abuja, a yau.

 

Mohammed Idris ya jaddada cewa kasafin kuɗin wannan shekarar ya mayar da hankali kan zuba jari a sassa masu muhimmanci da ke da tasiri na kai tsaye kan jin daɗi da ci gaban tattalin arzikin ƙasa.

 

“Kasafin kuɗi na 2025 ba kawai wata takarda ta kuɗi ba ce; yana nuna tsari mai ƙarfi na daidaita tattalin arziki da kwanciyar hankali a zamantakewa, da kuma cigaban ƙasa. Wannan kasafin ya maida hankali kan harkokin tsaro da ababen more rayuwa da ilimi da lafiya da ma’adinai da noma da wasu sassa masu matuƙar muhimmanci ga cigaban ƙasa.”

 

“Wannan shekara ta 2025, shekara ce ta tabbatar da sauye-sauyen da gwamnatin Shugaba Tinubu ta aiwatar, domin a fara jin ɗadin su a zahiri. Tuni muna gani a fili cewa farashin kayan abinci yana raguwa a hankali, wanda ke kawo sauƙi ga ‘yan ƙasa,” in ji shi.

 

Ministan ya tabbatar da cewa gwamnatin tarayya za ta tabbatar da aiwatar da kasafin kuɗi yadda ya kamata, tare da nuna gaskiya da riƙon amana wajen cimma burin shirin ”

 

“Ina tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa gwamnatin tarayya za ta ci gaba da aiki tuƙuru wajen aiwatar da wannan kasafin kuɗi domin cimma cikakken tasirinsa a rayuwar al’ummar mu. Don haka, ina kira ga duk ‘yan ƙasa su mara wa waɗannan ƙoƙari baya, domin mu gina Najeriya,” in ji shi.

 

Ministan ya yaba wa kafafen yaɗa labarai bisa jajircewarsu wajen kawo rahotanni kan taron, yana jaddada muhimmancinsu wajen yaɗa sahihan labarai da suka dace, ba tare da son rai ba, tare da mai da hankali kan ci gaban ƙasa.

 

Ya nanata cewa kafafen yaɗa labarai suna ba da gudunmuwa wajen tabbatar da dorewar dimokuraɗiyya da kuma tabbatar da cewa ‘yan Najeriya na samun ingantattun bayanai kan manyan tsare-tsaren sauyi da gwamnati ke aiwatarwa.

 

Mohammed Idris ya bayyana cewa dimokuraɗiyya tana bunƙasa ne ta hanyar tattaunawa bisa sani, fahimtar juna, da haɗin gwiwa don cigaban ƙasa. Saboda haka, ya yi kira ga kafafen yaɗa labarai da su ci gaba da kiyaye ƙa’idodin daidaito, alhaki, da ƙwarewa a cikin rahotanninsu.

 

“A wannan zamani da labaran ƙarya da son rai ke iya rinjayar tunanin jama’a cikin sauƙi, sadaukarwarku ga gaskiya da adalci ya fi zama mai muhimmanci fiye da da. Dole ne mu yi aiki tare don tabbatar da cewa bayanan da ke tsara ra’ayoyin jama’a sun dace da ainihin gaskiyar yadda ake tafiyar da mulki, ba tare da son rai ko ƙayatarwa maras tushe ba,” in ji shi.

 

Taron Minista karo na uku ya kuma samu halartar Ministan Masana’antu, Ciniki da Zuba Jari, Dakta Jumoke Oduwole, da Ministan kasa, Sanata John Owan Enoh.

 

Rel/Adamu Yusuf

Labarai

Labarai10 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara