Connect with us

Labarai

KAROTA Ta Sha Alwashin Ƙara Ƙarfafa Haɗin Kai da Jami’an Soji a Jihar Kano

Published

on

Daga Khadijah Aliyu 

Shugaban Hukumar Kula da Hanyoyi da Tsaron Ababen Hawa ta Jihar Kano,  (KAROTA), Faisal Mahmud Kabir, ya sake jaddada kudirinsa na inganta dangantaka mai kyau da haɗin kai da rundunonin soji da ke aiki a jihar Kano.

Faisal Mahmud ya sha alwashin hakan  ne yayin da ya karɓi baƙuncin Kwamandan 403 na makarantar horar da matukan jiragen sama da ke Kano, Group Captain Uchenna Ihediwa, a hedikwatar KAROTA.

Shugaban na KAROTA  ya amince cewa a wasu lokuta ana samun rashin fahimta tsakanin jami’an KAROTA da jami’an soji, amma ya tabbatar da cewa hukumar na aiki domin samar da hanyoyin warware duk wata takaddama cikin lumana.

Ya jaddada cewa burinsu shi ne tabbatar da kyakkyawar alaƙar aiki wadda za ta amfani jami’an tsaro da kuma al’umma baki ɗaya.

A nasa jawabin, Group Captain Uchenna Ihediwa ya ce ziyarar na da nufin ƙarfafa haɗin gwiwar da ke akwai tsakanin KAROTA da makarantar horas da matukan jiragen sojin sama, tare da mai da hankali kan tabbatar da doka da oda a hanyoyin jihar.

Ya jaddada muhimmancin haɗin kai, ƙwarewa, da kuma tsayawa tsayin daka ga dukkan jami’an tsaro domin tabbatar da kula da zirga-zirgar ababen hawa.

Kwamandan ya yabawa jami’an KAROTA bisa jajircewarsu da ƙwazon aikinsu, inda ya nuna buƙatar ci gaba da haɗin gwiwa tsakanin hukumomi domin inganta tsaron jama’a da kuma tabbatar da bin dokokin zirga-zirga.

 

 

Labarai

Ilimi15 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara