Connect with us

Labarai

Karamar Hukumar Birnin Kudu Za Ta Samar da Kekunan A-Daidaita-Sahu Don Zirga-zirgar Mata

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

An yi kira ga Gwamnatin Jihar Jigawa da ta dauki kwararan matakai don dakile dabi’ar sare bishiyoyi a fadin jihar.

Tsoho Gwamnan Jihar, Barrister Ali Sa’ad Birnin Kudu ya yi wannan kiran a lokacin taron muryar Birnin Kudu karo na 7 da aka gudanar a Birnin Kudu.

Barrister Ali Sa’ad Birnin Kudu

Ali Sa’ad Birnin Kudu wanda shi ne shugaban babban taron ya bukaci al’ummar garin Birnin Kudu da su mayar da hankali matuka ga al’amuran tsaro da ilimi da samarwa matasa ayyukan yi domin janye su daga tu’ammali da miyagun kwayoyi da sace sace.

Tun da farko a nasa jawabin, Shugaban riko na Muryar Birnin Kudu, Alhaji Ahmad Sa’id Kangire, ya ce kungiyar ta jagoranci bincike akan harkokin lafiya da ilimi tare da ci gaba da fafutukar kafa kwalejin ilimi ta musamman ta tarayya da kokarin kafa kananan ofisoshin ‘yan sanda a sassan garin Birnin Kudu.

Farfesa Muhammad Abubakar Birnin Kudu

Kangire, ya ce kungiyar ta kuma yi kokarin nemo mafita ga karancin ruwan sha da koyar da matasa sana’o’i domin kauwar da su daga miyagun dabi’u zuwa turbar dogaro da kai.

A jawabinsa, sakataren Gwamnatin jihar Malam Bala Ibrahim, ya bayyana taron a matsayin alamar da ke nuni da cewar Muryar Birnin Kudu ta samu karbuwa a wurin jama’a.

A don haka, ya ja hankalin daidaikun mutane su kasance masu bada gudummawa da mafi kankantar abin da suka mallaka da kuma karfinsu da shawara ta gari don cimma burin da aka sanya a gaba.

A nasa jawabin, shugaban karamar hukumar Birnin Kudu, Dr Builder Muhammad Uba, ya bada tabbacin samar da Keken A-Daidaita-Sahu domin zirga zirgar mata a cikin gari kamar yadda daya daga cikin mata da suka halarci taron ta mika koke.

Dangane da matsalar sare bishiyoyi barkatai kuwa, Dr. Builder Muhammad Uba ya ce karamar hukumar za ta dasa bishiyoyi milyan 2 domin amsa umarnin Gwamna Umari Namadi na daukar irin wannan mataki.

Cikin wadanda suka halarci taron, sun hada da Babban Malamin addinin musulunci, Farfesa Abubakar Sani Birnin Kudu da Abdullahi Garba Birnin kudu da masu rike da sarautu, da wasu daga cikin manyan jami’an gwamnati da masu ruwa da tsaki.

 

 

 

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara