Connect with us

Labarai

Karamar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Shugaban Karamar hukumar Birnin Kudu dake Jihar Jigawa, Dr. Builder Muhammad Uba ya kaddamar da sabbin shugabannin rikon kwarya na kungiyar ‘yan Achaba na yankin.

A Jawabin da ya gabatar a yayin kaddamarwar a fadar Hakimi, Dr Muhammad Uba yace an nada sabbin shugabanin ne domin samun zaman lafiya a tsakanin su.

Ya kuma hore su da su bi dokoki da ka’idojin kungiya, tare da baiwa Karamar hukumar hadin kai da goyan baya wajen kai rahotan zuwan bakin ‘yan achaba dan tabbatar da tsaro.

Builder Muhammed Uba ya ba su tabbacin samun hadin kai da goyan bayan Karamar hukumar, ya kuma nuna rashin jin dadi da yawan sace sacen babura a yankin.

Kazakika, ya yabawa Gwamna Umar Namadi bisa kokarin sa na tabbatar da tsaro.

Shi ma a nasa jawabin, Hakimin Birnin Kudu Alhaji Hussaini Hassan jibrin ya bada shawarar yiwa Babura lambobi domin samun saukin ganewa tare da basu horo dan kwarewa akan aikin achaba.

A jawaban su daban daban, Shugaban ‘yan achaba na jihar, Abbas Abdulkadir da sakataren kungiyar, Yau Muhammad sun yabawa shugaban karamar hukumar bisa daukar matakin nada shugabannin riko na kungiyar ‘yan achaba na yankin.

A jawabin sa na godiya, sabon shugaban rikon kungiyar ‘yan Achaba na yankin Auwalu Ibrahim ya bada tabbacin yin aiki bil hakki da gaskiya.

Labarai

Ilimi15 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara