Connect with us

Labarai

Karamar Hukumar B/Gwari Ta Kare Kasafin Kudinta A Majalisar Dokokin Jihar Kaduna

Published

on

Gwamnatin jihar Kaduna da karamar hukumar Birnin Gwari sun jaddada aniyarsu na karfafa hadin gwiwa domin kare rayuka da dukiyoyi a yankin.

Shugaban karamar hukumar Birnin Gwari Salisu Isah ya bayyana haka jim kadan bayan kare kudirin kasafin kudin shekarar 2026 da majalisar ta gabatar a gaban majalisar dokokin jihar Kaduna.

Alhaji Salisu Isah ya bayyana Birnin Gwari a matsayin wani yanki mai cike da tashin hankali da ke fuskantar kalubalen tsaro, inda ya jaddada bukatar gwamnati ta ci gaba da sanya ido a kai. Ya bayyana cewa majalisar ta gabatar da kasafin kudi sama da Naira biliyan 7 don inganta tsaro da samar da muhimman ababen more rayuwa a karamar hukumar da ta fi yawan masu noma.

A wani lamari makamancin haka, karamar hukumar Makarfi ta yi alkawarin ba da fifiko kan harkokin tsaro, ilimi, samar da lafiya da kuma ci gaban jama’a a kasafin kudi na shekarar 2026.

Shugaban karamar hukumar Garba Mohammed Sabon Gari ne ya bayyana haka a lokacin da yake kare kudirin kasafin kudin karamar hukumar a gaban kwamitin kasafin kudi da aiwatar da majalisar.

A cewarsa, majalisar ta ba da shawarar kashe sama da Naira biliyan 5 don inganta abubuwan more rayuwa da inganta zamantakewa da tattalin arziki a fadin yankin.

COV/SHAMSUDDEEN MANNIR ATIKU

Labarai

Labarai2 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai22 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara