Ilimi
Jigawa Ta Kebe Wuraren 57 don Kare Rikicin Manoma da Makiyaya
Gwamnatin jihar Jigawa ta ce daga cikin wuraren kiwo guda 400 da ke jihar, ta duba 57 domin dakile rikicin manoma da makiyaya a jihar.
Gwamna Umar Namadi ya bayyana haka ne a wajen bude taron tuntubar masu ruwa da tsaki kan sauye-sauyen kiwo tare da hadin gwiwa da kwamitin shugaban kasa na aiwatar da gyara harkokin kiwon dabbobi da aka gudanar a Dutse, babban birnin jihar.
Ya ce baya ga samar da tsarin doka na kare wuraren kiwo, manufar za ta kuma tabbatar da amfani da albarkatun kasa mai dorewa a jihar.
Gwamnan ya ce gwamnatin sa ta kuma dauki ma’aikatan kiwon lafiyar dabbobi 300 na al’umma domin su samar da ayyukan ci gaba ga manoma domin inganta harkar noma a jihar.
“Mun dauki aiki tare da horar da ma’aikatan kula da lafiyar dabbobi 300 na al’umma don gudanar da asibitocin kula da dabbobi ta wayar hannu guda 300 a fadin jihar kuma kawo yanzu ra’ayoyin da aka bayar kan hakan ya gamsar da su.
“Mun kuma yi wa dabbobi sama da dubu 560 allurar rigakafi a karkashin shirinmu na rigakafi na yau da kullun, muna ba su kariya daga cututtuka da kuma inganta sana’arsu.
“Wannan matakin ba wai kawai ya inganta kiwon dabbobi ba, har ma ya kara samar da kudin shiga ga manoman mu ta yadda kiyon dabbobi ya dore,” in ji Gwamnan.
Ya yi nuni da cewa ayyukan da gwamnatin jihar ke yi a fannin kiwo na ci gaba da samun sakamako mai kyau a kudurin kawo sauyi da inganta tasirinsa ga tattalin arzikin jihar.
“Yayin da muke shirin samar da ingantaccen tsari mai inganci na Kiwo ga Jiha, abin farin ciki ne a lura cewa ayyukan da muka yi a fannin kiwo sun ci gaba da samun sakamako mai kyau.
Namadi ya jaddada cewa, “Labarin nasarorin da muka samu wajen kafa ginshikin ci gaba mai dorewa sun hada da karfafa hanyoyin ganowa da wuri, da sassautawa da warware rikicin manoma da makiyaya tare da mai da hankali kan wuraren da ake samun matsala a tarihi,” Namadi ya jaddada.
Malam Umar Namadi ya yi alkawarin dorewar hadin gwiwa tsakanin hukumar manoma da makiyaya ta jihar Jigawa da kwamitin tsaro na masu ruwa da tsaki a bangarori da dama domin wanzar da zaman lafiya tsakanin manoma da makiyaya domin dorewar samar da ci gaba a fannin kiwo.
KARSHE/USMAN MZ
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
