Connect with us

Labarai

Jam’iyyar APC ta Zabi Sabbin Shugabanninta a Jihar Zamfara

Published

on

Daga Aminu Dalhatu 

Jam’iyyar APC ta gudanar da tarukan zaɓen shugabanni na mazabu da na ƙananan hukumomi cikin nasara a dukkan mazabu 147 da ƙananan hukumomi 14 na Jihar Zamfara, inda aka fitar da shugabannin jam’iyyar ta hanyar sulhu.

An gudanar da tarukan cikin kwanciyar hankali, kuma an bayyana su a matsayin masu tsari da nagarta, tare da halartar masu ruwa da tsaki da mambobin jam’iyyar daga sassa daban-daban na jihar.

Da yake zantawa da manema labarai a Gusau, shugaban kwamitin gudanar da tarukan, Babande Babakura Imam, ya ce an gudanar da aikin cikin nasara ba tare da wata tangarda ba.

Imam ya bayyana cewa tarukan na mazabu da ƙananan hukumomi sun samu halartar jama’a da yawa, inda aka sami dukkan shugabanni  ta hanyar  sulhu da amincewar mambobin jam’iyyar.

Ya ce, “Jami’an HukumarZabe mai Zaman Kanta ta kasa(INEC), da jami’an tsaro, da wakilan jam’iyyar APC daga sakatariyar ƙasa da ke Abuja, da kuma wakilan APC na jiha ne suka sanya ido kan yadda aka gudanar da tarukan.”

A cewarsa, tarukan ƙananan hukumomi sun fitar da shugabannin APC a dukkan ƙananan hukumomi 14, ciki har da shugabanni, sakatarori da sauran jami’ai.

Shi ma da yake jawabi, shugaban APC na Jihar Zamfara, Alhaji Tukur Danfulani, ya bayyana nasarar gudanar da tarukan a matsayin abin farin ciki ga jam’iyyar.

Danfulani ya yabawa kwamitin tarukan bisa bin ƙa’idojin jam’iyyar yadda ya kamata, wajen gudanar da aikin a duk faɗin jihar, yana mai jaddada cewa APC na da ƙudurin tabbatar da gaskiya da haɗin kai.

Shugaban jam’iyyar ya kuma nuna kwarin gwiwa cewa APC na da haɗin kai gabanin zaɓuka masu zuwa a jihar, yana mai cewa fitowar sabbin shugabanni zai ƙara ƙarfafa tsarin jam’iyyar.

Wannan ci gaba alama ce cewa APC ta shirya tsaf domin ƙwato jihar Zamfara tare da yin aiki domin sake zaɓen Bola Ahmed Tinubu da dukkan ‘yan takarar APC a zaɓen shekarar 2027,” in ji Danfulani.

Ya kuma bayyana gamsuwarsa da yadda mambobin jam’iyyar suka halarci tarukan da kuma yadda aka gudanar da su cikin tsari da lumana a faɗin jihar.

Labarai

Labarai2 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai22 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara