Ilimi
Jami’ar Ahmadu Bello Zaria Za Ta Horas Da ‘Yan Jarida Game Da Aikin Su
Shugaban jami’ar Ahmadu Bello da ke zaria, Farfesa Adamu Ahmed ya ce jami’ar za ta hada kai da kungiyar ‘yan jarida ta Najeriya domin horar da mambobinta.
Ya bayyana haka ne a lokacin da mambobin kungiyar NUJ reshen Zaria suka kai masa ziyarar taya murna a ofishin sa da ke Zariya.
Shugaban jami’ar wanda ya bayyana su a matsayin abokan jami’ar, ya kuma ce babu wata gwamnati da za ta yi kasa a gwiwa wajen hada kai da ‘yan jarida.
Ya ce abubuwa masu kyau suna faruwa a jami’ar Ahmadu Bello ba tare da sanin jama’a ba.
Shugaban ya yabawa kungiyar bisa wannan karramawar, inda ya ce ya ji dadin wakilcin su a zariya.
Da yake jawabi tun da farko, Shugaban kungiyar ‘yan jarida ta Najeriya reshen Zaria Malam Sagir Mohammed Awwal, wanda ya bayyana Farfesa Ahmed a matsayin mai kwazo, mai gaskiya da kirkire-kirkire, ya kuma taya ma’aikata da dalibai da daukacin tsofaffin daliban ABU murnar zaben Ahmed a matsayin shugaban kasa.
Sagir ya yabawa jami’ar bisa kyawun karatun ta, yana mai cewa gaggarumar gudumawar da take bayarwa wajen ci gaban Najeriya na da ban mamaki.
Ya ce an samu kyakyawar alaka tsakanin jami’ar da ‘yan jarida a zariya, kuma kungiyar na fatan samun kyakkyawar alaka.
Shugaban ya kuma ce mambobin kungiyar za su ci gaba da sauke nauyin da ya rataya a wuyansu na kwarewa wajen bunkasa harkokin ilimi a jami’ar.
Ya ce kungiyar na da mambobi 23 da suka gudanar da ayyuka a kananan hukumomi takwas na shiyyar Kaduna ta daya.
COV/HALIRU HAMZA
-
Labarai4 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai1 day agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai2 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai4 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
