Connect with us

Labarai

Jahar Kwara ta gudanar da gwajin Hawan jini, sukari ga Mutane dubu 102 Kauta

Published

on

Ma’aikatar lafiya ta jihar Kwara ta ce ta yi wa sama da mutane dubu dari da biyu (102,452) gwajin cutar hawan jini da ciwon suga a fadin kananan hukumomin jihar 16 daga watan Oktoba zuwa Disambar bara.

 

Kwamishiniyar lafiya ta jihar, Dakta Amina El-Imam, ta bayyana hakan a lokacin da take zantawa da manema labarai akan ayyukan ma’aikatar a Ilorin.

 

Ta ce an kuma ba da magungunan kyauta ga duk mutanen da aka sani da cutar hawan jini da ciwon sukari a lokacin motsa jiki.

 

Kwamishinar taa ce an sake horar da ma’aikatan kiwon lafiya a wuraren kiwon lafiya na matakin farko dana mataki na biyu da kuma manyan cibiyoyin lafiya game da wannan cuta.

 

Dakta El-Imam ta kuma ce an gudanar da aikin tantance cutar sankarar mama da mahaifa kyauta a fadin kananan hukumomi 16 na jihar a tsawon wannan lokaci.

 

Ta yi bayanin cewa an yi wa mata 1,151 da 807 gwajin cutar kansar nono da mahaifa, inda ta kara da cewa duk wadanda suka kamu da cutar suna karkashin  kulawa a asibitin koyarwa na jami’ar jihar (KWASUTH).

 

Kwamishinan ta lura cewa inganta kula da masu fama da tarin fuka ya haifar da nasarar samun maganin kashi 94 cikin 100 a shekarar data gabata ta 2024.

 

Ta ci gaba da cewa, an gudanar da ayyukan ba da magunguna kyauta a kan yara sama da 750,000 a makaranta da makarantun gwamnati da masu zaman kansu da kuma al’ummomi a fadin jihar.

 

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

 

Labarai

Labarai11 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara