Labarai
Hukumar Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa Ta Kai Samame Gidan Kakakin Majalisar Afrika Ta Kudu
Masu bincike sun kai samame gidan shugabar majalisar dokokin kasar Afrika ta Kudu, bisa zargin da ake mata na cin hanci da rashawa, wanda hakan ya sanya ‘yan adawa suka bukaci ta yi murabus.
Hakan dai na zuwa ne watanni biyu kafin babban zaben kasar, a dai-dai lokacin da ake ci gaba da kai wa ‘ya’yan jam’iyar da ke mulki ta ANC samame, bisa zarginsu da aikata badakalar cin hanci da rashawa.
Hukumar da ke yaki da cin hancin da rashawa ta kasar dai ta tabbatar da cewa, wata babbar tawagar jami’anta sun kai samamen ne don gudanar da binciken a gidan shugabar majalisar Nosiviwe Mapisa-Nqakula da ke Johannesburg.
Majalisar dokokin kasar dai ta ce wannan binciken da ake yi wa Mapisa-Nqakula, na da alaka da zargin badakala da ake mata lokacin ta na ministar tsaron kasar.
Mapisa-Nqakula ta rike mukamin ministar tsoron kasar ne tsakanin shekarar 2014 zuwa 2021, kafin daga bisani aka nadata kakakin majalisar dokokin kasar, da hakan ya fuskanci suka daga bangaren ‘yan adawa.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
