Connect with us

Labarai

Hukumar Kwastam Ta Kwace Kayayyaki na Sama da Naira Miliyan 82 A Bauchi

Published

on

Daga Alhassan Usman 

Sashen Ayyuka na Tarayya, da ke Yanki na 4 a Bauchi, na Hukumar Kwastam ta Najeriya (NCS) wato Zone D, ya kwace kayayyakin fasa-kwauri da darajar harajinsu ta kai sama da Naira Miliyan 82 cikin makonni biyu.

Kwamandan Yankin, Abdullahi Kaila, ya bayyana hakan yayin taron manema labarai a Bauchi, inda ya ce jami’an sashen yaki da fasa-kwauri sun yi nasarar kwace kayayyakin tsakanin ranakun  8 zuwa 19 ga watan Disamban 2025.

Ya bayyana cewa Sashen na Ayyukan Tarayya ne ke da alhakin aiwatar da dokokin Kwastam, bin manufofin haraji na gwamnati da kuma dakile fasa-kwauri a jihohi tara, wadanda suka hada da Adamawa, Taraba, Bauchi, Gombe, Borno, Yobe, Plateau, Benue da Nasarawa.

Kaila ya kara da cewa an kara karfafa ayyukan yaki da fasa-kwauri a yankin, ta hanyar inganta hadin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da masu sa ido, yana mai jaddada cewa irin wannan hadin gwiwar na kara musayar bayanan sirri da aiwatar da ayyukan hadin kai wajen yakar kungiyoyin fasa-kwauri.

Ya bukaci ‘yan kasuwa a yankin da su kasance masu bin doka, su kuma guji haramtaccen kasuwanci, yana mai gargadin cewa ba za a bar wata mafaka ga masu aikata fasa-kwauri ba.

Kwamandan ya kuma ce sashen zai ba da muhimmanci ga wayar da kan jama’a, ta hanyar amfani da kafafen yada labarai da kuma kai ziyara yankuna daban daban, domin fadakar da jama’a game da illar fasa-kwauri ga tattalin arziki da kuma karfafa su su rika kai rahoton haramtattun ayyuka.

Labarai

Ilimi15 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara