Connect with us

Labarai

Hukumar Alhazai ta Jigawa ta Jinjinawa Hukumomin Tsaro Bisa Goyon Bayan da Suke Ba Ta

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta yi kira ga Hukumar Shige da Fice ta kasa da ta tabbatar da gudanar da ayyuka cikin sauƙi da tsari ga maniyyatan Hajjin shekarar 2026 yayin tantance su a Filin Jirgin Sama na Nuhu Muhammadu Sunusi.

Babban Daraktan hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ne ya yi wannan kiran yayin wata ganawa da Kwanturolan Hukumar Shige da Fice ta jihar a hedikwatar hukumar da ke Dutse, babban birnin jihar.

Ya bayyana cewa an shirya taron ne domin tattauna tsare-tsare da dabarun da za su inganta matakan tsaro domin tunkarar ayyukan Hajjin shekarar 2026.

A cewarsa, samar da ingantattun na’urorin tantancewa da tsare-tsare masu sauƙi zai taimaka matuƙa wajen rage wahalar da maniyyata ke fuskanta tare da tabbatar da jigilarsu a kan lokaci domin gudanar da aikin Hajjin shekarar 2026.

Alhaji Ahmed Umar Labbo ya kuma yi kira ga hukumomin tsaro da sauran masu ruwa da tsaki da su ba da cikakken haɗin kai domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin maniyyata tun daga sansanin Alhazai har zuwa filin jirgin sama kafin tafiyarsu zuwa ƙasar Saudiyya.

Babban Daraktan ya gode wa dukkan hukumomin tsaro bisa ci gaba da goyon baya da haɗin kai domin cimma manufofin da ake buƙata.

A nasu jawabin, hukumomin tsaron sun tabbatar wa hukumar da cikakken goyon baya ga gwamnatin jihar.

Sun kuma yi alƙawarin taimakawa wajen samar da tsaro tare da tabbatar da jin daɗi da walwalar maniyyatan Hajji yayin gudanar da ayyukansu.

Labarai

Ilimi15 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara