Labarai
Hukumar Alhazai ta Jigawa ta Jinjinawa Hukumomin Tsaro Bisa Goyon Bayan da Suke Ba Ta
Daga Usman Muhammad Zaria
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta yi kira ga Hukumar Shige da Fice ta kasa da ta tabbatar da gudanar da ayyuka cikin sauƙi da tsari ga maniyyatan Hajjin shekarar 2026 yayin tantance su a Filin Jirgin Sama na Nuhu Muhammadu Sunusi.
Babban Daraktan hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ne ya yi wannan kiran yayin wata ganawa da Kwanturolan Hukumar Shige da Fice ta jihar a hedikwatar hukumar da ke Dutse, babban birnin jihar.
Ya bayyana cewa an shirya taron ne domin tattauna tsare-tsare da dabarun da za su inganta matakan tsaro domin tunkarar ayyukan Hajjin shekarar 2026.

A cewarsa, samar da ingantattun na’urorin tantancewa da tsare-tsare masu sauƙi zai taimaka matuƙa wajen rage wahalar da maniyyata ke fuskanta tare da tabbatar da jigilarsu a kan lokaci domin gudanar da aikin Hajjin shekarar 2026.
Alhaji Ahmed Umar Labbo ya kuma yi kira ga hukumomin tsaro da sauran masu ruwa da tsaki da su ba da cikakken haɗin kai domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin maniyyata tun daga sansanin Alhazai har zuwa filin jirgin sama kafin tafiyarsu zuwa ƙasar Saudiyya.
Babban Daraktan ya gode wa dukkan hukumomin tsaro bisa ci gaba da goyon baya da haɗin kai domin cimma manufofin da ake buƙata.

A nasu jawabin, hukumomin tsaron sun tabbatar wa hukumar da cikakken goyon baya ga gwamnatin jihar.
Sun kuma yi alƙawarin taimakawa wajen samar da tsaro tare da tabbatar da jin daɗi da walwalar maniyyatan Hajji yayin gudanar da ayyukansu.
-
Labarai3 days agoAdalci a Kauru LGA Yayin da Tsarin Raba Mukamai ke Kara Karɓuwa Domin Wakilci Nagari
-
Labarai5 days agoHukumar Alhazan Jihar Jigawa ta Kaddamar da Kwamitin Amirul Hajjin Bana
-
Labarai2 days agoRadio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya
-
Labarai7 days agoTrump Ya Aike da Daftarin Shirin Zaman Lafiya ga Iran
-
Labarai2 days agoMasarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin
-
Labarai2 days agoHukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana
-
Labarai5 days agoHajjin2026: Jigawa ta Kara Kaimi Wajen Horar Da Maniyyata
-
Labarai2 days agoƊaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano
