Connect with us

Labarai

Gwamnatin Neja Ta Haramtawa Motocin Da Suka Fito Daga Hanyar Maje Bin Gadar Dikko

Published

on

Gwamnatin Jihar Neja ta ba da umarnin hana motocin da suka  fito daga Maje hawa gadar Dikko.

Gwamnan jihar Mohammed Umar Bago ya ba da umarnin a lokacin da ya ziyarci wurin da wata tankar mai  ta yi  gobara a mahadar Dikko da ke karamar hukumar Gurara ta jihar Neja.

Gwamnan, wanda ya koka kan yadda wasu direbobi ke nuna halin ko-in-kula yayin tuki, ya ce ba a amince duk wata mota da ta fito daga Maje ta bi ta gadar Dikko ba, sai dai su bi karkashin gadar zagayo kan hanyarsu.

Ya kuma umurci babban kwamandan hukumar kiyaye hadurra ta tarayya da ya kafa rundunar tsaro a yankin domin tabbatar da aiwatar da wannan umarni, yayin da ya yi kira ga kungiyoyin sufuri da abin ya shafa da su ba hukumar kiyaye hadurra ta kasa hadin kai.

Sai dai Gwamnan ya bayyana fashewar tankar mai da ta yi sanadin mutuwar mutane da dama a matsayin abin tausayi tare da gode wa Allah da lamarin bai kai ga al’ummar da ke makwabtaka da su ba.

Umar Bago ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta gaggauta daukar matakin kammala aikin titin Minna zuwa Suleja domin jinkirin aikin hanyar yana haddasa asarar  rayuka da dukiyoyi.

Gwamnan ya godewa Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Jihar Neja, da Hukumar Kashe Gobara, da Hukumar kiyaye hadurra ta kasa, da Kungiyar Sufuri ta Kasa (NURT) da sauran hukumomin da suka bayar da gudunmawa wajen kawo dauki ga  wadanda fashewartankarya rutsa da su.

Ya ce za a kara  tura likitoci daga asibitocin da ke Minna domin su taimaka wajen kula da wadanda suka jikkata da ke samun kulawa a  babban asibitin Suleja.

Daga Aliyu Lawal

Labarai

Labarai12 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara