Connect with us

Labarai

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda 96 daga gwamnatin tarayya.

Kwamishinan Yada Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed ne ya bayyana hakan jim kaɗan bayan kammala taron Majalisar Zartarwa ta Jihar da aka gudanar a Fadar Gwamnati da ke Dutse.

A cewarsa, majalisar ta amince da sayen gidajen ne daga Ma’aikatar Gidaje da Raya Birane ta Tarayya.

Ya bayyana cewa sayen gidajen na da nufin magance matsalar matsuguni a cikin jihar, musamman ga ma’aikatan gwamnati da sauran waɗanda suka cancanta.

Ya ce shirin na daga cikin Ajandar Gwamna Umar Namadi 12, wadda ta ƙunshi babbar dabarar bunkasa gidaje da raya birane, domin samar da matsuguni mai kyau, rage gibin gidaje, da inganta rayuwar al’umma.

Wannan na daga cikin ƙoƙarin gwamnatin na faɗaɗa damar samun gidaje masu araha da kuma kyautata jin daɗin jama’a.

Ya kuma bayyana cewa majalisar ta amince da kashe sama da Naira miliyan 914 domin ƙarin ayyuka a kan aikin gina hanyar Chuwasu zuwa Chakwaikwaiwa zuwa Zango Maje, wadda za ta haɗa da hanyar Yan Dutse zuwa Chori.

Sagir ya ce ƙarin ayyukan sun zama wajibi bayan ƙarin binciken fasaha da bitar aikin da aka gudanar, domin ƙara inganta ƙarfinsa da tsarin magudanan ruwa.

Ya ce majalisar ta ce sauyin da aka yi a cikin tsarin aikin zai tabbatar da cewa aikin ya cika ƙa’idojin da ake buƙata, tare da biyan buƙatun zirga-zirgar al’ummomin da za su amfana da shi.

Kwamishinan ya ƙara da cewa, da wannan amincewar, jimillar kuɗin kwangilar aikin ta kai sama da Naira Biliyan 5.4. Yana mai cewa hanyar Chuwasu zuwa Chakwaikwaiwa zuwa Zango Maje muhimmiyar hanya ce ta karkara wadda aka tsara domin inganta haɗin kai tsakanin al’umma, sauƙaƙa jigilar amfanin gona,  ƙara samun damar isa kasuwanni, makarantu da cibiyoyin kiwon lafiya, tare da bunƙasa tattalin arziƙi a yankin da abin ya shafa.

Labarai

Labarai1 hour ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai23 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai2 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Mafi Shahara