Ilimi
Gwamnatin Jigawa Za Ta Kafa Cibiyoyin Bada Abincin Buda Baki A Manyan Makarantu
Gwamnatin Jihar Jigawa za ta kafa cibiyoyin bada abincin buda baki a manyan makarantun jihar guda 10, domin tallafa wa dalibai a lokacin azumi.
Kwamishinan yada labarai, matasa, wasanni da al’adu na jihar Alhaji Sagir Musa Ahmed ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai sakamakon taron majalisar zartaswar jihar da aka gudanar a gidan gwamnati na Dutse.
A cewarsa, gwamnatin jihar na shirin ciyar da mutane sama da miliyan uku da dubu dari takwas a watan Ramadan na bana domin tallafawa gajiyayyu da marasa galihu.
Alhaji Sagir Musa Ahmed ya yi nuni da cewa, gwamnatin jihar ta amince da naira kusan miliyan dubu dari uku domin ciyar a watan Ramadan a cibiyoyi 609 da aka kafa a fadin jihar.
Ya ce shirin tallafin da aka tsara ya yi daidai da manufofin gwamnati na rage wahalhalu ga marasa galihu musamman a wannan lokaci na da ake ciki.
Kwamishinan ya kara da cewa, majalisar ta kuma amince da kafa kwamitin wucin gadi a dukkanin kananan hukumomi 27, wanda kwamishinan kananan hukumomi ko kuma manyan mashawarta na musamman a kananan hukumomin za su jagoranta domin tabbatar da gaskiya.
Sagir Musa ya ce, sauran mambobin kwamitin sun hada da ‘yan majalisar dokokin jihar, mataimaka na musamman, shugabannin kananan hukumomi da DPO na ‘yan sanda.
Sauran sun hada da jami’in tsaro na DSS na karamar hukumar, wakilin hakimai, da sakataren karamar hukuma wanda zai zama sakataren kwamitin.
Hakazalika majalisar ta kuma amince da sama da Naira Biliyan daya da miliyan 125 don ƙarin siyan kayan abinci da za a raba ga marasa galihu, a ƙoƙarin da ake yi na rage wahalhalun rayuwa.
Usman Muhammad Zaria
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
