Connect with us

Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Sha Alwashin Bin Kadin Shari’ar Walida Abdulhadi

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria 

Gwamna Umar Namadi ya tabbatar da cewa Gwamnatin  Jigawa za ta bi sawun shari’ar sace ‘yar asalin jihar, Walida Abdulhadi, har zuwa ƙarshe, tare da tabbatar da an yi adalci.

Gwamnan ya bayar da wannan tabbaci ne a ranar Laraba lokacin da ya gana da iyayen Walida tare da lauyansu a Fadar Gwamnati da ke Dutse.

A yayin ganawar, gwamnan ya yi wa iyayen bayani kan halin da Walida ke ciki a halin yanzu, tare da jaddada ƙudirin gwamnati na tabbatar da kula da lafiyar ta, ci gaba da karatunta da kuma kula da walwalarta gaba ɗaya.

Ya bayyana cewa a halin yanzu Walida na karɓar kulawar jinya a wani asibiti da Gwamnatin Jigawa ke ɗaukar nauyin kuɗaɗensa, yana mai cewa bayan kammala wannan kulawa, za a mayar da ita cikin iyalanta.

Gwamnan ya kuma bayyana cewa an riga an tura ƙwararrun ma’aikatan kula da walwalar al’umma domin ba Walida da jaririnta kulawa ta musamman, yana mai jaddada cewa an tanadi dukkan matakan tallafi da suka dace domin kare lafiyarta da tabbatar da ganin ta murmure.

Bugu da ƙari, Gwamna Namadi ya ce gwamnatin jihar za ta mayar da Walida makaranta tare da ɗaukar nauyin karatunta gaba ɗaya domin ta ci gaba da neman ilimi ba tare da wata tangarda ba.

Da yake bayyana lamarin a matsayin satar mutane kai tsaye, gwamnan ya sha alwashin cewa gwamnatin jihar za ta tabbatar da an yi adalci ta hanyoyin shari’a da suka dace, kuma duk wanda aka samu da laifi za a hukunta shi bisa doka.

Haka kuma ya sanar da cewa gwamnati za ta tallafa wa Walida da iyalanta domin inganta rayuwarsu da taimaka musu su sake farfaɗo da rayuwarsu.

Gwamna Namadi ya sake nanata ƙudirin Gwamnatin Jihar Jigawa na kare haƙƙoƙi da mutuncin dukkan ‘yan jihar a duk inda suke.

Da yake magana a madadin iyayen Walida, lauyanta Barrista Kabiru Adamu ya gode wa Gwamna Namadi bisa saurin ɗaukar matakin ceto yarinyar da kuma ƙoƙarin gwamnati na ganin an dawo da martabar ta.

Labarai

Labarai44 minutes ago

Ramadan: Sarkin Kauru Ya Bukaci a Kara Karfafa Tsoro Tare da Tallafawa Marasa Galihu

Daga Yusuf Zubairu Kauru Sarkin Kauru da ke Jihar Kaduna, Alhaji Zakari Ya’u Shehu Usman, ya yi kira da a...

Labarai1 hour ago

Gwamnatin Jigawa Ta Sha Alwashin Bin Kadin Shari’ar Walida Abdulhadi

Daga Usman Muhammad Zaria  Gwamna Umar Namadi ya tabbatar da cewa Gwamnatin  Jigawa za ta bi sawun shari’ar sace ‘yar...

Labarai1 day ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi1 day ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai1 day ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai2 days ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai3 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai3 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai3 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Mafi Shahara