Connect with us

Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kasafin 2026

Published

on

Daga Aminu Dalhatu 

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya sanya hannu kan dokar Kasafin Kuɗin Shekarar 2026, bayan Majalisar Dokokin Jihar Zamfara ta amince da shi.

An gudanar da bikin sanya hannun ne a Fadar Gwamnati da ke Gusau.

Sai dai a wajen taron, gwamnan bai bayyana jimillar adadin kasafin kuɗin shekarar ta 2026 ba.

Tun a ranar 4 ga watan Disamba ne Gwamna Dauda Lawal ya gabatar da kasafin kuɗi da ya haura naira biliyan 861 na shekarar 2026 ga Majalisar Dokokin Jihar Zamfara domin amincewa.

Manyan jami’an da suka halarci taron sun haɗa da Mataimakin Gwamnan Jihar Zamfara, Mani Malam Mumini; Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Zamfara, Bilyaminu Isma’il Moriki; Sakataren Gwamnatin Jihar (SSG); Shugaban Ma’aikata (Chief of Staff); kwamishinoni da sauran manyan jami’an gwamnati.

 

A baya, Majalisar Dokokin Jihar Zamfara ta riga ta amince da Kudirin Kasafin Kuɗin 2026 ya zama doka, bayan gabatar da rahoton Kwamitin Majalisar kan Kuɗi da Kasafi.

Kudirin ya tanadi jimillar kasafin kuɗi na naira biliyan 871.337 domin shekarar  2026.

Yayin gabatar da rahoton kwamitin, Shugaban Kwamitin, Rilwanu Marafa Na Gambo, ya bayyana cewa dukkan Ma’aikatun Gwamnati, Hukumomi da Cibiyoyi (MDAs) a jihar sun bayyana gaban kwamitin tare da kare kasafin kuɗinsu. Ya ƙara da cewa an samu gagarumin ci gaba a tsarin samun kuɗaɗen shiga na yawancin hukumomi.

Na Gambo ya kuma bayyana cewa kwamitin ya ba da shawarar ƙara naira biliyan 8 domin ayyukan ci gaba (capital expenditure) a Ma’aikatar Kananan Hukumomi da Harkokin Sarauta, tare da ƙara naira biliyan 2 domin kuɗaɗen gudanarwa (recurrent expenditure) ga Majalisar Dokokin Jihar Zamfara.

A lokacin amincewa da kudirin, Shugaban Majalisar, Bilyaminu Isma’il Moriki, ya ce Majalisar ta yi la’akari da manyan abubuwan da ya kamata gwamnati ta fi bai wa fifiko yanzu, da suka haɗa da tsaro, noma, lafiya, ilimi da gine-gine.

Ya ce an tsara kasafin kuɗin ne domin ya dace da buƙatu da muradun al’umma a matakin ƙananan hukumomi da sauran fannoni, tare da tabbatar da daidaiton kasafi da mai da hankali sosai kan adalci da haɗa kowa da kowa.

Labarai

Labarai2 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai22 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara