Labarai
Gwamnan Kwara Ya Yabawa Shugaba Tinubu
Gwamna AbdulRazaq ya yabawa Shugaba Tinubu yayin da Sojoji suka tura cikakken birgediya domin fatattakar masu garkuwa da mutane daga dazukan Kwara.
Hedkwatar sojojin Najeriya ta aika da cikakken birgediya da manyan kayan aiki a sassa daban-daban na Kwara ta Kudu, domin rage matsalolin tsaro a yankin.
Wata sanarwa da sakataren yada labarai gwamnan, Rafiu Ajakaye ya fitar ta ce Tuni dai sojojin suka yi ta luguden wuta ta cikin kauyukan Oke Ode da Babanla, dukkansu a karamar hukumar Ifelodun.
Har ila yau, rundunar ta kara da cewa, aikin ya zarce zuwa Edu da Patigi domin ratsa dazuzzukan da masu garkuwa da mutane suka fara kai hare-hare na matsorata a kan al’ummomi daban-daban tare da yin garkuwa da mutane domin neman kudin fansa.
Ta ce Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq, ya gana da Shugaba Bola Tinubu a ziyarar da ya kai a Jos.
Ta yabawa shugaban kasa bisa wannan goyon baya, da kuma babban hafsan soji da jami’an tsaro na hadin gwiwa bisa sabon matakin kawar da duk wata barazana ga lafiyar jama’a a jihar.
A kwanakin baya ne hedkwatar rundunar ta umarci babban hafsan sojin kasa na GOC 2 Manjo Janar CR Nnebeife da ya koma Kwara domin gudanar da ayyukan dawo da zaman lafiya a yankin.
Ya kuma yabawa ofishin mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, babban hafsan soji, babban hafsan soji na 2, da duk wani jami’in tsaro.
REL/ALI MUHAMMAD RABIU
-
Labarai4 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai2 days agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai6 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai5 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
